< Ƙidaya 12 >

1 Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
Là Marie et Aaron firent querelle à Moïse au sujet de la femme Éthiopienne qu'il avait épousée; car il avait pris pour femme une Éthiopienne.
2 Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
Et ils dirent: N'est-ce que par Moïse seul que l'Éternel parle? n'est-ce pas aussi par nous qu'il parle? Et l'Éternel entendit.
3 (Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
Or cet homme-là, Moïse, était le plus doux des humains qui sont sur la face de la terre.
4 Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
Sur-le-champ l'Éternel dit à Moïse, et à Aaron et à Marie: Allez tous trois vous présenter à la Tente du Rendez-vous; et ils allèrent tous trois.
5 Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
Alors l'Éternel descendit dans la colonne de nuée, et se tenant à la porte de la Tente Il appela Aaron et Marie, et ils parurent tous deux.
6 sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
Et Il dit: Entendez mes paroles! S'il existe parmi vous un prophète, moi l'Éternel, je me révèle à lui par la vision: c'est dans un songe que je lui parle.
7 Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
Il n'en est pas ainsi de mon serviteur Moïse: il est l'homme de confiance dans toute ma Maison.
8 Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
Je m'abouche avec lui, en Personne, et sans déguisement; il voit la face de l'Éternel. Comment donc ne craignez-vous pas de faire querelle à mon serviteur Moïse?
9 Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
Ainsi s'enflamma contre eux la colère de l'Éternel qui s'éloigna; et la nuée se retira aussi de la Tente,
10 Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
et voilà que Marie avait une lèpre comme la neige; et Aaron se tourna vers Marie, et voilà qu'elle avait la lèpre!
11 sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
Alors Aaron dit à Moïse: Je t'en conjure, mon seigneur, ne mets pas sur nous le poids du péché que nous avons commis dans notre folie, et dont nous sommes coupables.
12 Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
Oh! qu'elle ne soit pas comme le mort-né qui en sortant du sein maternel a le corps à demi détruit.
13 Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
Alors Moïse cria vers l'Éternel et dit: O Dieu! oh! guéris-la donc!
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
Et l'Éternel dit à Moïse: Mais si son père avait craché à sa face, ne serait-elle pas sept jours dans l'opprobre?… Elle sera séquestrée sept jours hors du camp; après quoi elle sera réintégrée.
15 Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
Marie fut donc séquestrée sept jours hors du camp, et le peuple ne partit point avant la réintégration de Marie.
16 Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.
Et après cela le peuple partit de Hathseroth et vint camper au désert de Paran.

< Ƙidaya 12 >