< Ƙidaya 12 >

1 Miriyam da Haruna suka fara zargin Musa saboda matarsa’yar ƙasar Kush da ya aura.
And Miriam speaks—Aaron also—against Moses concerning the circumstance of the Cushite woman whom he had taken, for he had taken a Cushite woman;
2 Suka ce, “Ubangiji ya yi magana ta wurin Musa ne kaɗai? Ashe, bai yi magana ta wurinmu mu ma ba?” Ubangiji kuwa ya ji wannan.
and they say, “Has YHWH only spoken by Moses? Has he not also spoken by us?” And YHWH hears.
3 (Musa kuwa mutum ne mai tawali’u ƙwarai, mafi tawali’u fiye da kowane mutum a duniya.)
And the man Moses [is] very humble, more than any of the men who [are] on the face of the ground.
4 Nan da nan Ubangiji ya ce wa Musa, da Haruna da kuma Miriyam, “Ku fita ku tafi Tentin Sujada, dukanku uku.” Sai dukansu uku suka tafi.
And YHWH suddenly says to Moses, and to Aaron, and to Miriam, “Come out, you three, to the Tent of Meeting”; and those three come out.
5 Sai Ubangiji ya sauko a cikin ginshiƙin girgije; ya tsaya a bakin ƙofar Tenti, ya kira Haruna da Miriyam. Sa’ad da su biyu suka gusa gaba,
And YHWH comes down in the pillar of the cloud, and stands at the opening of the tent, and calls Aaron and Miriam, and both of them come out.
6 sai ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa, “Duk lokacin da akwai annabin Ubangiji a cikinku, nakan bayyana kaina gare shi cikin wahayi, in yi magana da shi cikin mafarkai.
And He says, “Now hear My words: If your prophet is of YHWH, I make Myself known to him in a vision; I speak with him in a dream.
7 Amma ba haka nake magana da Musa bawana ba; na sa shi yă lura da dukan jama’ata Isra’ila.
Not so My servant Moses; He [is] steadfast in all My house.
8 Da shi nake magana fuska da fuska, a fili kuma, ba a kacici-kacici ba; yakan ga siffar Ubangiji. To, me ya sa ba ku ji tsoro ku yi magana a kan bawana Musa ba?”
I speak with him mouth to mouth, Even [by] an appearance, and not in riddles; And he beholds the form of YHWH attentively. Now why have you not been afraid To speak against My servant—against Moses?”
9 Sai fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kansu, ya kuma rabu da su.
And the anger of YHWH burns against them, and He goes on,
10 Da girgijen ya tashi daga bisa Tentin, sai ga Miriyam tsaye, kuturwa, fari fat. Haruna kuwa ya juya wajenta ya ga ta kuturce;
and the cloud has turned aside from off the tent, and behold, Miriam [is] leprous as snow; and Aaron turns to Miriam, and behold, leprous!
11 sai Haruna ya ce wa Musa, “Ranka yă daɗe, ina roƙonka kada ka hukunta mu, gama zunubin da muka yi, mun yi ne cikin wauta.
And Aaron says to Moses, “O my lord, please do not lay [this] sin on us [in] which we have been foolish, and [in] which we have sinned;
12 Kada ka sa ta zama kamar haifaffen mataccen jariri daga cikin mahaifiya wanda rabin jikin ruɓaɓɓe ne.”
please do not let her be as [one] dead, when in his coming out from the womb of his mother—the half of his flesh is consumed.”
13 Saboda haka sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Allah, ina roƙonka ka warkar da ita!”
And Moses cries to YHWH, saying, “O God, please give healing to her! Please!”
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata miyau a fuskarta, ashe, ba za tă ji kunya har kwana bakwai ba? A fitar da ita bayan sansani kwana bakwai; bayan haka za a iya dawo da ita.”
And YHWH says to Moses, “But [if] her father had but spat in her face—is she not ashamed [for] seven days? She is shut out [for] seven days at the outside of the camp, and afterward she is gathered.”
15 Haka aka fitar da Miriyam bayan sansani kwana bakwai, mutane kuwa ba su ci gaba da tafiya ba sai da aka dawo da ita.
And Miriam is shut out at the outside of the camp [for] seven days, and the people have not journeyed until Miriam is gathered;
16 Bayan haka sai mutane suka bar Hazerot suka sauka a Hamadan Faran.
and afterward the people have journeyed from Hazeroth, and they encamp in the wilderness of Paran.

< Ƙidaya 12 >