< Nehemiya 6 >
1 Sa’ad da magana ta zo kunnen Sanballat, da Tobiya, da Geshem mutumin Arab da kuma sauran abokan gābanmu cewa na sāke gina katangar har babu sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake har zuwa lokacin ban sa ƙofofi a ƙyamare ba
And when Sanballat, and Tobiah, and Geshem the Arabian, and the rest of our enemies heard that I had built the wall, and that there were no more breaches therein, (though at that time I had not set vp the doores vpon the gates)
2 Sanballat da Geshem suka aika mini wannan saƙo cewa, “Ka zo, mu sadu a wani ƙauye a filin Ono.” Amma makirci ne suke yi don su cuce ni;
Then sent Sanballat and Geshem vnto me, saying, Come thou that we may meete together in the villages in the plaine of Ono: and they thought to doe me euill.
3 saboda haka sai na aika musu da wannan amsa, na ce, “Ina cikin babban aiki, ba zan kuwa iya gangarawa ba. Don me zan bar aikin yă tsaya don in gangara zuwa wurinku?”
Therefore I sent messengers vnto them, saying, I haue a great worke to doe, and I can not come downe: why should the worke cease, whiles I leaue it, and come downe to you?
4 Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā.
Yet they sent vnto me foure times after this sort. And I answered them after the same maner.
5 Sai sau na biya, Sanballat ya aiki mataimakinsa gare ni da irin saƙo guda, kuma a hannunsa akwai wasiƙar da ba a yimƙe ba
Then sent Sanballat his seruant after this sorte vnto me the fift time, with an open letter in his hand,
6 wadda aka rubuta cewa, “An ba da labari cikin al’ummai, kuma Geshem ya ce gaskiya ne, cewa kai da Yahudawa kun shirya tawaye, saboda haka kuke sāke ginin katangar. Ban da haka ma, bisa ga waɗannan rahotanni kana shirin zaman sarkinsu
Wherein was written, It is reported among the heathen, and Gashmu hath sayd it, that thou and the Iewes thinke to rebel, for the which cause thou buildest the wall and thou wilt bee their King according to these wordes.
7 har ma ka naɗa annabawa su yi wannan shela game da kai a Urushalima, su ce, ‘Akwai sarki a Yahuda!’ To, wannan rahoto zai koma wurin sarki; saboda haka ka zo, mu tattauna wannan batu.”
Thou hast also ordeyned the Prophets to preach of thee at Ierusalem, saying, There is a King in Iudah: and nowe according to these wordes it shall come to the Kings eares: come now therefore, and let vs take counsell together.
8 Sai na aika masa wannan amsa, na ce, “Babu wani abu haka da yake faruwa; ka dai ƙaga wannan daga tunaninka ne.”
Then I sent vnto him, saying, It is not done according to these wordes that thou sayest: for thou feynest them of thine owne heart.
9 Suka dai yi ƙoƙari su tsoratar da mu, suna cewa, “Hannuwansu za su rasa ƙarfin yin aiki, ba kuwa za su ƙare aikin ba.” Amma na yi addu’a na ce, “Yanzu, ya Allah, ka ƙarfafa hannuwana.”
For all they afrayed vs, saying, Their handes shalbe weakened from the worke, and it shall not be done: nowe therefore incourage thou me.
10 Wata rana na tafi gidan Shemahiya ɗan Delahiya, ɗan Mehetabel, wanda aka hana fita a gidansa. Ya ce mini, “Mu sadu gobe a gidan Allah, a cikin haikali, mu kuma kulle ƙofofin haikali, gama mutane suna zuwa su kashe ka, tabbatacce za su zo da dare su kashe ka.”
And I came to the house of Shemaiah the sonne of Delaiah the sonne of Mehetabeel, and he was shut vp, and he said, Let vs come together into the house of God in the middes of the Temple, and shut the doores of the Temple: for they will come to slay thee: yea, in the night will they come to kill thee.
11 Amma na ce, “Ya kamata mutum kamar ni yă gudu? Ko kuwa ya kamata wani kamar ni yă shiga cikin haikali don yă ceci ransa? Ba zan tafi ba!”
Then I said, Should such a man as I, flee? Who is he, being as I am, that would go into the Temple to liue? I will not goe in.
12 Na gane cewa Allah bai aike shi ba, ya yi annabci a kaina domin Tobiya da Sanballat sun yi hayarsa ne.
And loe, I perceiued, that God had not sent him, but that he pronounced this prophecie against me: for Tobiah and Sanballat had hired him.
13 An yi hayarsa don yă sa in ji tsoro in yi zunubi ta yin haka, sa’an nan za su ba ni mugun suna, su wofinta ni.
Therefore was he hyred, that I might be afrayde, and doe thus, and sinne, and that they might haue an euill report that they might reproche me.
14 Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat, saboda abin da suka yi; ka kuma tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawa waɗanda suke ƙoƙari su tsorata ni.
My God, remember thou Tobiah, and Sanballat according vnto these their workes, and Noadiah the Prophetesse also, and the rest of the Prophets that would haue put me in feare.
15 Cikin kwana hamsin da biyu aka gama gina katangar, a ranar ashirin da biyar ga watan Elul.
Notwithstanding the wall was finished on the fiue and twentieth day of Elul, in two and fiftie dayes.
16 Sa’ad da dukan abokan gābanmu suka ji haka, dukan al’umman da suke kewaye da mu suka ji tsoro, suka rasa ƙarfin halinsu, domin sun gane cewa wannan aiki an yi shi da taimakon Allahnmu ne.
And when all our enemies heard thereof, euen all the heathen that were about vs, they were afraid, and their courage failed them: for they knew, that this worke was wrought by our God.
17 A waɗannan kwanaki, manyan garin Yahuda suka yi ta aika wasiƙu masu yawa zuwa ga Tobiya, shi kuma ya yi ta aika musu da amsoshi.
And in these dayes were there many of the princes of Iudah, whose letters went vnto Tobiah, and those of Tobiah came vnto them.
18 Gama mutane da yawa a cikin Yahuda sun rantse wa Tobiya za su goyi bayansa, domin ya auri’yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato, Yehohanan, ya auri’yar Meshullam, ɗan Berekiya.
For there were many in Iudah, that were sworne vnto him: for he was the sonne in lawe of Shechaniah, the sonne of Arah: and his sonne Iehonathan had the daughter of Meshullam, the sonne of Berechiah.
19 Ban da haka ma, mutanen sun yi ta ba ni labarin ayyuka masu kyau da Tobiya ya yi, sa’an nan kuma suna faɗa masa duk abin da na faɗa. Tobiya kuwa ya aika wasiƙu don yă tsorata ni.
Yea, they spake in his praise before me, and tolde him my wordes, and Tobiah sent letters to put me in feare.