< Nahum 2 >

1 Mai hari yana matsowa a kanki, Ninebe. Ki tsare mafaka, ki yi gadin hanya ki sha ɗamara ki tattaro dukan ƙarfinki!
A maul is come up before thy face; guard the defences, watch the way, make thy loins strong, fortify thy power mightily! —
2 Ubangiji zai maido da darajar Yaƙub, kamar ta Isra’ila, ko da yake masu washewa sun washe su suka kuma lalatar da inabinsu.
For the LORD restoreth the pride of Jacob, as the pride of Israel; for the emptiers have emptied them out, and marred their vine-branches. —
3 Garkuwoyin sojojinsa ja wur ne; jarumawansa suna sanye da kaya masu ruwan jan garura. Ƙarafan kekunan yaƙi suna walƙiya a ranar da aka shirya su; ana kaɗa māsu da bantsoro.
The shield of his mighty men is made red, the valiant men are in scarlet; the chariots are fire of steel in the day of his preparation, and the cypress spears are made to quiver.
4 Kekunan yaƙi sun zabura a tituna, suna kai da kawowa a dandali. Suna walƙiya kamar tocila suna sheƙawa a guje kamar walƙiya.
The chariots rush madly in the streets, they jostle one against another in the broad places; the appearance of them is like torches, they run to and fro like the lightnings.
5 Ninebe ta tattara rundunarta, duk da haka sun yi ta tuntuɓe a kan hanyarsu. Sun ruga zuwa katangan birnin, sun sanya garkuwar kāriya a inda ya kamata.
He bethinketh himself of his worthies; they stumble in their march; they make haste to the wall thereof, and the mantelet is prepared.
6 An buɗe ƙofofin rafuffukan sai wurin ya rurrushe.
The gates of the rivers are opened, and the palace is dissolved.
7 An umarta cewa birnin za tă tafi bauta, za a kuma yi gaba da su. Bayi’yan mata suna kuka kamar tattabaru suna buga ƙirjinsu.
And the queen is uncovered, she is carried away, and her handmaids moan as with the voice of doves, tabering upon their breasts.
8 Ninebe tana kama da tafki, wanda ruwanta yana yoyo. Suna kuka suna cewa, “Ku tsaya! Ku tsaya,” amma ba wanda ya waiga.
But Nineveh hath been from of old like a pool of water; yet they flee away; 'Stand, stand'; but none looketh back.
9 A washe azurfa; a washe zinariya; dukiyarsu ba ta da iyaka, arzikinsu kuma ba ya ƙarewa.
Take ye the spoil of silver, take the spoil of gold; for there is no end of the store, rich with all precious vessels.
10 Ta zama wofi, an washe ta, an tuɓe ta! Zukata sun narke, gwiwoyi suna kaɗuwa, jikuna suna rawa, fuskoki duk sun kwantsare!
She is empty, and void, and waste; and the heart melteth, and the knees smite together, and convulsion is in all loins, and the faces of them all have gathered blackness.
11 Ina kogon zakokin nan yake yanzu, inda suka ciyar da’ya’yansu, inda zaki da zakanya sukan shiga, da’ya’yansu, ba mai damunsu
Where is the den of the lions, which was the feeding-place of the young lions, where the lion and the lioness walked, and the lion's whelp, and none made them afraid?
12 Zaki ya kashe abin da ya ishe’ya’yansa ya kuma murɗe wuyan dabbobi ya cika wurin zamansa da abin da ya kama ya cika kogwanninsa da abin da ya kashe.
The lion did tear in pieces enough for his whelps, and strangled for his lionesses, and filled his caves with prey, and his dens with ravin.
13 “Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ƙone kekunan yaƙinki, takobi kuma zai fafare’ya’yan zakokinki. Ba kuma zan bar miki namun jejin da za ki kashe a duniya ba. Ba kuwa za a ƙara jin muryar’yan saƙonki ba.”
Behold, I am against thee, saith the LORD of hosts, and I will burn her chariots in the smoke, and the sword shall devour thy young lions; and I will cut off thy prey from the earth, and the voice of thy messengers shall no more be heard.

< Nahum 2 >