< Mika 6 >
1 Ku saurari abin da Ubangiji ya ce, “Tashi ku gabatar da ƙararku a gaban duwatsu; bari tuddai su ji abin da kuke so ku faɗa.
Écoutez donc la parole: Le Seigneur, le Seigneur a dit: Lève-toi, annonce le jugement aux montagnes, et que les collines entendent ta voix!
2 “Ku saurara, ya ku duwatsu game da tuhumar da Ubangiji yake muku, ku ji, ku daɗaɗɗun tushin duniya. Gama Ubangiji yana da ƙara a kan mutanensa; yana tuhumar Isra’ila.
Écoutez, montagnes, le jugement du Seigneur, et vous aussi, vallées, fondements de la terre; car le Seigneur vient en jugement devant Son peuple, et Il plaidera avec Israël.
3 “Ya ku mutanena, me na yi muku? Ta yaya na nawaita muku? Ku amsa mini.
Mon peuple, que t'ai-Je fait? En quoi t'ai-Je contristé? En qui t'ai-Je déplu? Réponds-Moi.
4 Na fito da ku daga ƙasar Masar na kuma’yantar da ku daga ƙasar bauta. Na aika da Musa yă jagorance ku, haka ma Haruna da Miriyam.
Est-ce parce que Je t'ai fait sortir de la terre d'Égypte, que Je t'ai affranchi de la maison de servitude, et que J'ai envoyé devant toi Moïse, Aaron et Marie?
5 Ya ku mutanena, ku tuna abin da Balak sarkin Mowab ya ƙulla da kuma amsar da Bala’am ɗan Beyor ya bayar. Ku tuna da tafiyarku daga Shittim zuwa Gilgal, don ku san ayyukan adalcin Ubangiji.”
Mon peuple, souviens-toi donc de ce qu'a médité contre toi Balac, roi de Moab, et de la réponse que lui a rapportée Balaam, fils de Béor, depuis Sétim jusqu'à Galgala, afin que l'on connût la justice du Seigneur.
6 Da me zan zo a gaban Ubangiji in rusuna a gaban Maɗaukaki Allah? Shin, zan zo ne a gabansa da hadaya ta ƙonawa, da ɗan maraƙi bana ɗaya?
Comment prendrai-je le Seigneur? Comment serai-je agréable à mon Dieu très-haut? Le prendrai-je par des holocaustes, par des veaux d'un an?
7 Ubangiji zai ji daɗin hadayar raguna dubbai da kuma rafuffukan mai dubbai goma? Zan ba da ɗan farina ne don laifina, ko’ya’yan jikina domin zunubin raina?
Le Seigneur accueillera-t-Il des milliers de béliers, des myriades de chèvres grasses? Donnerai-je, pour mes impiétés, les premiers-nés de mes troupeaux, et, pour les péchés de mon âme, le fruit de mes entrailles?
8 Ya nuna maka, ya mutum, abin da yake mai kyau. Me Ubangiji yake bukata daga gare ka kuwa shi ne ka yi gaskiya ka so aikata jinƙai ka kuma yi tafiya da tawali’u a gaban Allah.
Ô homme, faut-il te dire ce qui est bon? Est-ce que le Seigneur demande de toi quelque chose, sinon que tu pratiques la justice, que tu aimes la miséricorde, et que tu sois prêt à cheminer avec le Seigneur ton Dieu?
9 Ku saurara! Ubangiji yana kira ga birni, a ji tsoron sunana kuwa hikima ce, “Ku kasa kunne ga sandan nan da kuma wannan wanda ya naɗa.
La voix du Seigneur sera invoquée dans la ville, et sauvera ceux qui craignent Son Nom. Écoute, tribu: Qui donc mettra l'ordre en ta cité?
10 Har yanzu zan manta, ya muguwar gida da dukiyarki da kika samu a muguwar hanya zan kuma manta da bugaggen mudun awo wanda ake zargi?
Est-ce le feu? Est-ce la maison de l'impie amassant des trésors iniques, avec une insolente impiété?
11 Zan kuɓutar da mutumin da yake da ma’auni na rashin gaskiya, da kuma buhun ma’aunan ƙarya?
Sera-t-il absous, l'homme injuste avec ses fausses balances et ses faux poids en un sac?
12 Attajiranta masu fitina ne; mutanenta kuma maƙaryata ne harsunansu kuwa suna yaudara.
Car c'est ainsi que ceux qui demeurent dans la ville ont amassé leurs richesses impies; et ils ne disent que des mensonges, et dans leur bouche leur langue s'est enorgueillie.
13 Saboda haka, zan hallaka ku in lalace ku saboda zunubanku.
Et Moi Je commencerai par te frapper, et Je t'effacerai à cause de tes crimes.
14 Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba, cikinku zai zama babu kome Za ku tattara amma ba za ku yi ajiyar kome ba, gama abin da kuka yi ajiya zan ba wa takobi.
Tu mangeras, et ne seras point rassasié, et il y aura sur toi des ténèbres; et le Seigneur Se détournera; tu ne seras point sauvée; et ceux qui échapperont seront livrés au glaive.
15 Za ku yi shuki amma ba za ku girba ba; za ku matse zaitun amma ba za ku yi amfani da mai wa kanku ba, za ku tattaka’ya’yan inabi amma ba za ku sha ruwan inabin ba.
Tu sèmeras et ne moissonneras pas; tu pressureras l'olive, et tu ne seras pas oint de son huile; tu pressureras la grappe, et tu n'en boiras pas le vin; et les lois de Mon peuple seront abolies.
16 Kuna kiyaye ƙa’idodin Omri da dukan ayyukan gidan Ahab kun kuma bi al’adunsu. Saboda haka, zan maishe ku kufai in mai da ku abin dariya a cikin mutane, za ku sha reni a wurin al’ummai.”
Car tu as gardé les ordonnances de Zambri, et toutes les œuvres de la maison d'Achab; et tu as marché dans toutes leurs voies, pour que Je te livre, toi, à la destruction et aux sifflets de tes habitants; et vous recueillerez les opprobres des peuples.