< Mika 4 >
1 A kwanakin ƙarshe za a kafa dutsen haikalin Ubangiji yă zama babba a cikin duwatsu. Za a ɗaga shi sama da tuddai, mutane kuma za su riƙa ɗunguma zuwa gare shi.
In the last days, the mountain where the Lord's Temple stands will be recognized as the highest of all mountains, rising above other hills. Crowds of people from many places will travel to it.
2 Al’ummai da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, don mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Doka za tă fita daga Sihiyona, maganar Ubangiji kuma daga Urushalima.
Many nations will come and say, “Let's go up to the mountain of the Lord, to the Temple of the God of Jacob. There God will teach us his ways and we will follow his directions.” God's teachings will spread out from Zion, his word from Jerusalem.
3 Zai shari’anta tsakanin mutane yă kuma sulhunta tsakanin manyan al’ummai nesa da kuma kusa. Har su mai da takubansu su zama garemani, māsunsu kuma su zama wuƙaƙen askin itace. Al’umma ba za tă ɗauki takobi gāba da wata al’umma ba, ko a yi horarwa don yaƙi.
The Lord will decide the cases of the nations, he will settle arguments between distant powerful nations. They will hammer their swords and turn them into plough blades, and their spears into pruning hooks. Nations will not fight against each other anymore; they will no longer learn methods of warfare.
4 Kowa zai zauna a tushen kuringar inabinsa da tushen ɓaurensa, kuma ba wanda zai tsoratar da su, gama Ubangiji Maɗaukaki ne ya faɗa.
Everyone will be able to sit under their own vine and their own fig tree, for there will be no one to make them afraid. I the Lord Almighty has spoken!
5 Dukan al’ummai za su iya tafiya a cikin sunan allolinsu; mu dai za mu yi tafiya a cikin sunan Ubangiji Allahnmu har abada abadin.
Even though all the other nations follow their gods, we will follow the Lord our God forever and ever.
6 “A wannan rana,” in ji Ubangiji, “zan tattara guragu; zan kuma tara masu zaman bauta, da waɗanda na sa suka damu.
On that day, declares the Lord, I will gather those who are lame, I will bring together those who have been scattered in exile, those whom I punished.
7 Zan mai da guragu su zama raguwa, waɗanda aka kora, su zama al’umma mai ƙarfi. Ubangiji zai yi mulkinsu a Dutsen Sihiyona daga wannan rana da kuma har abada.
I will make those who remain, crippled and driven far away, into a strong nation, and the Lord will rule them from Mount Zion forever and ever.
8 Game da ke, ya hasumiyar tsaron garke, Ya mafaka Diyar Sihiyona, za a maido miki da mulkinki na dā, sarauta kuma za tă zo wa Diyar Urushalima.”
And as for you, Jerusalem, watchtower of the flock, your former royal rule and power will be returned to you: the kingdom will be given back to Jerusalem.
9 Don me yanzu kike kuka da ƙarfi, ba ki da sarki ne? Masu shawararki sun hallaka ne, da zafi ya cika ki kamar mace mai naƙuda?
So why are you screaming aloud? Don't you have a king? Has the king who advises you died so that pain has gripped you like a woman in childbirth?
10 Ki yi birgima cikin zafin azaba, ya Diyar Sihiyona, kamar macen da take naƙuda, don yanzu dole ki bar birni ki kafa sansani a filin Allah. Za ki tafi Babilon; a can za a kuɓutar da ki. A can ne Ubangiji zai fanshe ki daga hannun maƙiyanki.
Thrash around in agony like a woman giving birth, people of Zion—for you will be expelled from the city, forced to camp out in the open, and exiled to Babylon. But the Lord will bring you back, and rescue you from the power of your enemies.
11 Amma yanzu al’ummai da yawa suna gāba da ke. Suna cewa, “Bari a ƙazantar da ita, bari mu zuba wa Sihiyona ido.”
Right now many enemies are gathered against you, saying, “Let us attack and violate her, so we can look with gloating over Zion!”
12 Amma ba su san tunanin Ubangiji ba; ba su fahimci shirinsa ba, shi da ya tattara su kamar dammuna a masussuka.
But they don't know what the Lord is thinking, and don't understand what he is planning. He has brought them together like bundles of grain to the threshing floor.
13 “Ki tashi ki yi sussuka, ya Diyar Sihiyona, gama zan ba ki ƙahonin ƙarfe; zan ba ki kofatan tagulla domin ki ragargaje al’ummai masu yawa.” Za ki ba Ubangiji dukan dukiyarsu da suka tara ta hanyar zamba, wadatarsu kuma ga Ubangiji dukan duniya.
People of Zion, get up and start threshing, for I will make for you iron horns and bronze hooves so you can break many nations into pieces. You will present their stolen plunder to the Lord, their wealth to the Lord of all the earth.