< Mika 1 >

1 Maganar Ubangiji ta zo wa Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da kuma na Hezekiya, sarakunan Yahuda, Mika ya ga wahayi a kan Samariya da kuma a kan Urushalima. Ga abin da ya ce.
The word of the Lord, that came vnto Micah the Morashite in the dayes of Iotham, Ahaz, and Hezekiah Kings of Iudah, which he sawe concerning Samaria, and Ierusalem.
2 Ku ji, ya ku mutane duka, ki saurara, ya ke duniya da dukan mazauna cikinki, bari Ubangiji Mai Iko Duka yă zama shaida a kanku, daga haikalinsa mai tsarki.
Heare, al ye people: hearke thou, O earth, and all that therein is, and let the Lord God be witnes against you, euen ye Lord from his holy Teple.
3 Duba! Ubangiji yana zuwa daga wurin zamansa; zai sauko yă taka maɗaukakan wuraren duniya.
For beholde, the Lord commeth out of his place, and will come downe, and tread vpon the hie places of the earth.
4 Duwatsu za su narke a ƙarƙashin ƙafafunsa, kamar kaki a gaban wuta, kwaruruka kuma za su ɓace, kamar ruwan da yake gangarowa daga tsauni.
And the mountaines shall melt vnder him (so shall the valleys cleaue) as waxe before the fire, and as the waters that are powred downewarde.
5 Duk wannan zai faru saboda laifin Yaƙub, da kuma zunuban gidan Isra’ila ne. Mene ne laifin Yaƙub? Shin, ba Samariya ba ce? Ina ne maɗaukakan wuraren Yahuda? Shin, ba Urushalima ba ce?
For the wickednes of Iaakob is all this, and for the sinnes of the house of Israel: what is the wickednes of Iaakob? Is not Samaria? and which are the hie places of Iudah? Is not Ierusalem?
6 “Saboda haka zan mai da Samariya tarin juji, wurin noman inabi. Zan zubar da duwatsunta a cikin kwari in kuma bar harsashin gininta a bayyane.
Therefore I wil make Samaria as an heape of the fielde, and for the planting of a vineyard, and I will cause the stones thereof to tumble downe into the valley, and I will discouer the foundations thereof.
7 Za a ragargaje dukan allolinta; za a ƙone dukan baye-bayenta na haikali da wuta; zan lalatar da dukan gumakanta. Tun da ta wurin karuwanci ne ta tattara su, ga karuwanci kuma za su koma.”
And all the grauen images thereof shalbe broken, and all the giftes thereof shalbe burnt with the fire, and all the idoles thereof will I destroy: for she gathered it of the hire of an harlot, and they shall returne to the wages of an harlot.
8 Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka; zan yi tafiya ba takalmi, zan tuɓe, in kuma yi tafiya tsirara. Zan yi kuka kamar dila, in yi baƙin ciki kamar mujiya.
Therefore I will mourne and howle: I wil goe without clothes, and naked: I will make lamentation like the dragons, and mourning as the ostriches.
9 Gama raunin Samariya ba mai warkewa ba ne; ya bazu har Yahuda. Ya ma kai bakin ƙofar mutanena, har ma Urushalima da kanta.
For her plagues are grieuous: for it is come into Iudah: the enemie is come vnto the gate of my people, vnto Ierusalem.
10 Kada a faɗe shi a Gat; kada ma a yi kuka. A maimako haka, a yi birgima a cikin ƙura a Bet-Leyafra.
Declare ye it not at Gath, neither weepe ye: for the house of Aphrah roule thy selfe in the dust.
11 Ku wuce tsirara da kuma kunya, ku mazaunan Shafir. Bet-Ezel tana makoki domin babu wani daga Za’anan da ya fito don yă taimaka.
Thou that dwellest at Shaphir, go together naked with shame: she that dwelleth at Zaanan, shall not come forth in ye mourning of Beth-ezel: the enemie shall receiue of you for his standing.
12 Mazaunan Marot sun ƙosa su ga alheri, amma Ubangiji ya sauko da azaba, har zuwa ƙofar Urushalima.
For the inhabitant of Maroth wayted for good, but euill came from the Lord vnto the gate of Ierusalem.
13 Ku da kuke zama a Lakish, ku ɗaura wa dawakai kekunan yaƙi. Gama ku kuka fara yin zunubi a Sihiyona, gama an sami laifofin Isra’ila a cikinku.
O thou inhabitant of Lachish, binde the charet to the beastes of price: she is the beginning of the sinne to the daughter of Zion: for the transgressions of Israel were found in thee.
14 Saboda haka za ku ba da kyautan bankwana ga Moreshet Gat. Garin Akzib zai zama abin yaudara ga sarakunan Isra’ila.
Therefore shalt thou giue presents to Moresheth Gath: the houses of Achzib shalbe as a lye to the Kings of Israel.
15 Ku mazaunan Maresha Ubangiji zai kawo wanda zai ci ku da yaƙi. Sarakunan Isra’ila za su gudu zuwa Adullam.
Yet will I bring an heire vnto thee, O inhabitant of Mareshah, he shall come vnto Adullam, the glorie of Israel.
16 Ku aske kanku ƙwal don makoki, ku yi wa kanku ƙwalƙwal kamar ungulu. Gama za a ja’ya’yan da kuke farin ciki a kai su bauta.
Make thee balde: and shaue thee for thy delicate children: enlarge thy baldenesse as the eagle, for they are gone into captiuity from thee.

< Mika 1 >