< Mattiyu 9 >

1 Yesu ya shiga jirgin ruwa, ya ƙetare ya zo garinsa.
Og han gik om Bord i et Skib og for over og kom til sin egen By.
2 Waɗansu mutane suka kawo masa wani shanyayye, kwance a tabarma. Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Kada ka damu saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
Og se, de bare til ham en værkbruden, som laa paa en Seng; og da Jesus saa deres Tro, sagde han til den værkbrudne: „Søn! vær frimodig, dine Synder forlades dig.”
3 Da jin wannan, waɗansu malaman dokoki suka ce wa juna, “Wannan mutum yana yin saɓo!”
Og se, nogle af de skriftkloge sagde ved sig selv: „Denne taler bespotteligt.”
4 Sane da tunaninsu, Yesu ya ce, “Me ya sa kuke da mugun tunani a zuciyarku?
Og da Jesus saa deres Tanker, sagde han: „Hvorfor tænke I ondt i eders Hjerter?
5 Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuwa a ce, ‘Tashi ka yi tafiya?’
Thi hvilket er lettest at sige: Dine Synder forlades dig, eller at sige: Staa op og gaa?
6 Amma don ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya yă gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
Men for at I skulle vide, at Menneskesønnen har Magt paa Jorden til at forlade Synder,” da siger han til den værkbrudne: „Staa op, og tag din Seng, og gaa til dit Hus!”
7 Mutumin kuwa ya tashi ya tafi gida.
Og han stod op og gik bort til sit Hus.
8 Da taron suka ga haka, sai suka cika da tsoro, suka yabi Allah wanda ya ba wa mutane irin ikon nan.
Men da Skarerne saa det, frygtede de og priste Gud, som havde givet Menneskene en saadan Magt.
9 Da Yesu ya yi gaba daga wurin, sai ya ga wani mutum mai suna Mattiyu zaune a inda ake karɓar haraji. Ya ce masa, “Bi ni.” Mattiyu kuwa ya tashi ya bi shi.
Og da Jesus gik videre derfra, saa han en Mand, som hed Matthæus, sidde ved Toldboden; og han siger til ham: „Følg mig!” Og han stod op og fulgte ham.
10 Yayinda Yesu yake cin abinci a gidan Mattiyu, masu karɓar haraji da yawa da kuma masu zunubi suka zo suka kuwa ci tare da shi da kuma almajiransa.
Og det skete, da han sad til Bords i Huset, se, da kom der mange Toldere og Syndere og sade til Bords med Jesus og hans Disciple.
11 Sa’ad da Farisiyawa suka ga haka, sai suka tambayi almajiransa suka ce, “Don me malaminku yake ci tare da masu karɓar haraji, da masu zunubi?”
Og da Farisæerne saa det, sagde de til hans Disciple: „Hvorfor spiser eders Mester med Toldere og Syndere?”
12 Da jin wannan, Yesu ya ce, “Ai, ba masu lafiya ba ne su bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
Men da Jesus hørte det, sagde han: „De raske trænge ikke til Læge, men de syge.
13 Amma ku je ku koyi abin da wannan yake nufi, ‘Jinƙai nake bukata, ba hadaya ba.’Gama ban zo domin in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi.”
Men gaar hen og lærer, hvad det vil sige: Jeg har Lyst til Barmhjertighed og ikke til Offer; thi jeg er ikke kommen for at kalde retfærdige, men Syndere.”
14 Sai almajiran Yohanna suka zo suka tambaye shi suka ce, “Me ya sa mu da Farisiyawa muke azumi, amma almajiranka ba sa yi?”
Da komme Johannes's Disciple til ham og sige: „Hvorfor faste vi og Farisæerne meget, men dine Disciple faste ikke?”
15 Yesu ya amsa ya ce, “Yaya baƙin ango za su yi makoki yayinda yake tare da su? Lokaci yana zuwa da za a ɗauke ango daga gare su, sa’an nan za su yi azumi.
Og Jesus sagde til dem: „Kunne Brudesvendene sørge, saa længe Brudgommen er hos dem? Men der skal komme Dage, da Brudgommen bliver tagen fra dem, og da skulle de faste.
16 “Ba mai yin faci da sabon ƙyalle a kan tsohuwar riga, gama facin zai kece rigar yă sa kecewar ma ta fi ta dā muni.
Men ingen sætter en Lap af uvalket Klæde paa et gammelt Klædebon; thi Lappen river Klædebonnet itu, og der bliver et værre Hul.
17 Mutane kuma ba sa zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In suka yi haka, salkunan za su farfashe, ruwan inabin kuwa yă zube salkunan kuma su lalace. A’a, ai, sukan zuba sabon ruwan inabi ne a cikin sababbin salkuna, don a kiyaye dukan biyun.”
Man kommer heller ikke ung Vin paa gamle Læderflasker, ellers sprænges Læderflaskerne, og Vinen spildes, og Læderflaskerne ødelægges; men man kommer ung Vin paa nye Læderflasker, saa blive begge Dele bevarede.”
18 Yayinda yake faɗin wannan, sai wani mai mulki ya zo ya durƙusa a gabansa ya ce, “Yanzu-yanzu diyata ta rasu. Amma ka zo ka ɗibiya hannunka a kanta, za tă kuwa rayu.”
Medens han talte dette til dem, se, da kom der en Forstander og faldt ned for ham og sagde: „Min Datter er lige nu død; men kom og læg din Haand paa hende, saa bliver hun levende.”
19 Yesu ya tashi ya tafi tare da shi, haka ma almajiransa.
Og Jesus stod op og fulgte ham med sine Disciple.
20 A daidai wannan lokaci sai ga wata mace wadda ta yi shekaru goma sha biyu tana zub da jini ta raɓo ta bayansa ta taɓa gefen rigarsa.
Og se, en Kvinde, som havde haft Blodflod i tolv Aar, traadte hen bagfra og rørte ved Fligen af hans Klædebon;
21 Ta ce a ranta, “Ko da rigarsa ce kawai na taɓo, zan warke.”
thi hun sagde ved sig selv: „Dersom jeg blot rører ved hans Klædebon, bliver jeg frelst.”
22 Yesu ya juya ya gan ta. Sai ya ce, “Kada ki damu diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke.” Nan take macen ta warke.
Men Jesus vendte sig om, og da han saa hende, sagde han: „Datter! vær frimodig, din Tro har frelst dig.” Og Kvinden blev frelst fra den samme Time.
23 Da Yesu ya shiga gidan mai mulkin ya ga masu busan sarewa da taro mai hayaniya,
Og da Jesus kom til Forstanderens Hus og saa Fløjtespillerne og Hoben, som larmede, sagde han:
24 sai ya ce, “Ku ba da wuri. Ai, yarinyar ba tă mutu ba, tana barci ne.” Amma suka yi masa dariya.
„Gaar bort, thi Pigen er ikke død, men hun sover.” Og de lo ad ham.
25 Bayan an fitar da taron waje, sai ya shiga ciki ya kama yarinyar a hannu, ta kuwa tashi.
Men da Hoben var dreven ud, gik han ind og tog hende ved Haanden; og Pigen stod op.
26 Labarin wannan kuwa ya bazu ko’ina a yankin.
Og Rygtet herom kom ud i hele den Egn.
27 Da Yesu ya fita daga can, sai waɗansu makafi biyu suka bi shi, suna kira, suna cewa, “Ka yi mana jinƙai, Ɗan Dawuda!”
Og da Jesus gik bort derfra, fulgte der ham to blinde, som raabte og sagde: „Forbarm dig over os, du Davids Søn!”
28 Da ya shiga cikin gida, sai makafin nan suka zo wurinsa, ya kuma tambaye su, “Kun gaskata cewa ina iya yin wannan?” Suka amsa suka ce, “I, Ubangiji.”
Men da han kom ind i Huset, gik de blinde til ham; og Jesus siger til dem: „Tro I, at jeg kan gøre dette?” De sige til ham: „Ja, Herre!”
29 Sa’an nan ya taɓa idanunsu ya ce, “Bisa ga bangaskiyarku a yi muku haka”;
Da rørte han ved deres Øjne og sagde: „Det ske eder efter eders Tro!”
30 sai idanunsu suka buɗe. Yesu ya gargaɗe su sosai ya ce, “Ku lura kada wani yă san wani abu game da wannan.”
Og deres Øjne bleve aabnede. Og Jesus bød dem strengt og sagde: „Ser til, lad ingen faa det at vide.”
31 Amma suka fita suka yi ta baza labari game da shi ko’ina a wannan yankin.
Men de gik ud og udbredte Rygtet om ham i hele den Egn.
32 Yayinda suke fitowa, sai aka kawo wa Yesu wani mutum mai aljani, da ba ya iya magana.
Men da disse gik ud, se, da førte de til ham et stumt Menneske, som var besat.
33 Sa’ad da aka fitar da aljanin kuwa, sai beben ya yi magana. Taron suka yi mamaki suka ce, “Ba a taɓa ganin irin wannan abu a Isra’ila ba.”
Og da den onde Aand var uddreven, talte den stumme. Og Skarerne forundrede sig og sagde: „Aldrig er saadant set i Israel.”
34 Amma Farisiyawa suka ce, “Ai, da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
Men Farisæerne sagde: „Ved de onde Aanders Fyrste uddriver han de onde Aander.”
35 Yesu ya zazzaga dukan garuruwa da ƙauyuka, yana koyarwa a majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin yana kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.
Og Jesus gik omkring i alle Byerne og Landsbyerne, lærte i deres Synagoger og prædikede Rigets Evangelium og helbredte enhver Sygdom og enhver Skrøbelighed.
36 Da ya ga taron mutane, sai ya ji tausayinsu, domin an wulaƙanta su ba su kuma da mai taimako, kamar tumaki marasa makiyayi.
Men da han saa Skarerne, ynkedes han inderligt over dem; thi de vare vanrøgtede og forkomne som Faar, der ikke have Hyrde.
37 Sai ya ce wa almajiransa, “Girbi yana da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne.
Da siger han til sine Disciple: „Høsten er stor, men Arbejderne ere faa;
38 Saboda haka ku roƙi Ubangijin girbi, yă aiko da ma’aikata cikin gonarsa na girbi.”
beder derfor Høstens Herre om, at han vil sende Arbejdere ud til sin Høst.”

< Mattiyu 9 >