< Mattiyu 8 >

1 Da ya sauko daga dutsen, sai taron mutane mai yawan gaske suka bi shi.
Et quand il fut descendu de la montagne, de grandes troupes le suivirent.
2 Wani mutum mai kuturta ya zo ya durƙusa a gabansa ya ce, “Ubangiji, in kana so, kana iya tsabtacce ni.”
Et voici, un lépreux vint et se prosterna devant lui, en lui disant: Seigneur, si tu veux, tu peux me rendre net.
3 Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin. Ya ce, “Ina so, ka tsabtacce!” Nan da nan aka warkar da shi daga kuturtarsa.
Et Jésus étendant la main, le toucha, en disant: je le veux, sois net; et incontinent sa lèpre fut guérie.
4 Sai Yesu ya ce masa, “Ka lura kada ka gaya wa kowa. Sai dai ka tafi, ka nuna kanka ga firist ka kuma yi bayarwar da Musa ya umarta, a matsayin shaida gare su.”
Puis Jésus lui dit: prends garde de ne le dire à personne; mais va, et te montre au Sacrificateur, et offre le don que Moïse a ordonné, afin que cela leur serve de témoignage.
5 Da Yesu ya shiga Kafarnahum, sai wani jarumi ya zo wurinsa, yana neman taimako.
Et quand Jésus fut entré dans Capernaüm, un Centenier vint à lui, le priant,
6 Ya ce, “Ubangiji, bawana yana kwance a gida shanyayye, yana kuma shan azaba ƙwarai.”
Et disant: Seigneur, mon serviteur est paralytique dans ma maison, et il souffre extrêmement.
7 Yesu ya ce masa, “Zan je in warkar da shi.”
Jésus lui dit: j'irai, et je le guérirai.
8 Jarumin ya amsa, “Ubangiji, ban cancanci in sa ka zo gidana ba, ka dai yi magana kawai, bawana zai warke.
Mais le Centenier lui répondit: Seigneur, je ne suis pas digne que tu entres sous mon toit; mais dis seulement la parole, et mon serviteur sera guéri.
9 Gama ni kaina mutum ne a ƙarƙashin iko, da kuma sojoji a ƙarƙashina. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi; wancan kuma, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan ce wa bawana, ‘Yi wannan,’ sai kuwa yă yi.”
Car moi-même qui suis un homme [constitué] sous la puissance [d'autrui], j'ai sous moi des gens de guerre, et je dis à l'un: va, et il va; et à un autre: viens, et il vient; et à mon serviteur: fais cela, et il le fait.
10 Da Yesu ya ji wannan, sai ya yi mamaki ya kuma ce wa waɗanda suke binsa, “Gaskiya nake gaya muku, ban taɓa samun wani a Isra’ila da bangaskiya mai girma haka ba.
Ce que Jésus ayant entendu, il s'en étonna, et dit à ceux qui le suivaient: en vérité, je vous dis que je n'ai pas trouvé, même en Israël, une si grande foi.
11 Ina kuma gaya muku da yawa za su zo daga gabas da kuma yamma, su ɗauki wuraren zamansu a biki tare da Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub a cikin mulkin sama.
Mais je vous dis que plusieurs viendront d'Orient et d'Occident, et seront à table dans le Royaume des cieux, avec Abraham, Isaac et Jacob.
12 Amma za a jefar da’ya’yan mulki waje, zuwa cikin baƙin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”
Et les enfants du Royaume seront jetés dans les ténèbres de dehors, où il y aura des pleurs et des grincements de dents.
13 Sa’an nan Yesu ya ce wa jarumin, “Je ka! Za a yi bisa ga bangaskiyarka.” A daidai wannan lokaci bawansa kuwa ya warke.
Alors Jésus dit au Centenier: va, et qu'il te soit fait selon que tu as cru. Et à l'heure même son serviteur fut guéri.
14 Da Yesu ya zo cikin gidan Bitrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance a gado tana da zazzaɓi.
Puis Jésus étant venu dans la maison de Pierre, vit la belle-mère de [Pierre] qui était au lit, et qui avait la fièvre.
15 Ya taɓa hannunta sai zazzaɓin ya sake ta, ta kuwa tashi ta fara yin masa hidima.
Et lui ayant touché la main, la fièvre la quitta; puis elle se leva, et les servit.
16 Da yamma ta yi, aka kawo masa masu aljanu da yawa, ya kuwa fitar da ruhohin ta wurin magana, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya.
Et le soir étant venu, on lui présenta plusieurs démoniaques, desquels il chassa par sa parole les esprits [malins], et guérit tous ceux qui se portaient mal.
17 Wannan ya faru ne domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa, “Ya ɗebi rashin lafiyarmu, ya kuma ɗauki cututtukanmu.”
Afin que fût accompli ce dont il avait été parlé par Esaïe le Prophète, en disant: il a pris nos langueurs, et a porté nos maladies.
18 Da Yesu ya ga taron mutane kewaye da shi, sai ya ba da umarni a ƙetare zuwa ɗayan hayin tafkin.
Or Jésus voyant autour de lui de grandes troupes, commanda de passer à l'autre rivage.
19 Sai wani malamin dokoki ya zo wurinsa ya ce, “Malam, zan bi ka duk inda za ka.”
Et un Scribe s'approchant, lui dit: Maître, je te suivrai partout où tu iras.
20 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”
Et Jésus lui dit: les renards ont des tanières, et les oiseaux du ciel ont des nids; mais le Fils de l'homme n'a pas où il puisse reposer sa tête.
21 Sai wani almajiri ya ce masa, “Ubangiji, da farko bari in je in binne mahaifina.”
Puis un autre de ses Disciples lui dit: Seigneur, permets-moi d'aller premièrement ensevelir mon père.
22 Amma Yesu ya ce masa, “Ka bi ni, ka bar matattu su binne matattunsu.”
Et Jésus lui dit: suis-moi, et laisse les morts ensevelir leurs morts.
23 Sai ya shiga jirgin ruwa, almajiransa kuwa suka bi shi.
Et quand il fut entré dans la nacelle, ses Disciples le suivirent.
24 Ba zato ba tsammani, sai wani babban hadari ya taso a tafkin, har raƙuman ruwan suka sha kan jirgin. Amma Yesu yana barci.
Et voici, il s'éleva sur la mer une si grande tempête que la nacelle était couverte de flots; et Jésus dormait.
25 Almajiran suka je suka tashe shi, suna cewa, “Ubangiji, ka cece mu! Za mu nutse!”
Et ses Disciples vinrent, et l'éveillèrent, en lui disant: Seigneur, sauve-nous, nous périssons!
26 Ya amsa ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, me ya sa kuke tsoro haka?” Sa’an nan ya tashi ya tsawata wa iskar da kuma raƙuman ruwan, sai wuri ya yi tsit gaba ɗaya.
Et il leur dit: pourquoi avez-vous peur, gens de petite foi? Alors s'étant levé il parla fortement aux vents et à la mer, et il se fit un grand calme.
27 Mutanen suka yi mamaki suka ce, “Wane irin mutum ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa suna masa biyayya!”
Et les gens [qui étaient là] s'en étonnèrent, et dirent: qui est celui-ci que les vents même et la mer lui obéissent?
28 Da ya isa ɗayan gefen a yankin Gadarenawa (ko kuwa Gerasenawa), sai ga mutum biyu masu aljanu suna fitowa daga kaburbura suka tarye shi. Su abin tsoro ne ƙwarai, har ba mai iya bin wannan hanya.
Et quand il fut passé à l'autre côté, dans le pays des Gergéséniens, deux démoniaques étant sortis des sépulcres le vinrent rencontrer, et [ils étaient] si dangereux que personne ne pouvait passer par ce chemin-là.
29 Suka yi ihu suka ce, “Me ya haɗa ka da mu, Ɗan Allah?” Ka zo ne nan don ka ji mana kafin lokaci yă yi?
Et voici, ils s'écrièrent, en disant: qu'y a-t-il entre nous et toi, Jésus Fils de Dieu? Es-tu venu ici nous tourmenter avant le temps?
30 Nesa kaɗan da su kuwa akwai babban garken aladu da yake kiwo.
Or il y avait un peu loin d'eux un grand troupeau de pourceaux qui paissait.
31 Aljanun suka roƙi Yesu suka ce, “In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan.”
Et les démons le priaient, en disant: si tu nous jettes dehors, permets-nous de nous en aller dans ce troupeau de pourceaux.
32 Ya ce musu, “Ku tafi!” Sai suka fita suka shiga cikin aladun, dukan garken kuwa ya gangara a guje daga kan tudun zuwa cikin tafkin aladun kuma suka mutu a cikin ruwa.
Et il leur dit: allez. Et eux étant sortis s'en allèrent dans le troupeau de pourceaux; et voilà, tout ce troupeau de pourceaux se précipita dans la mer, et ils moururent dans les eaux.
33 Masu kiwon aladun suka ruga, suka je cikin gari suka ba da labarin dukan wannan, haɗe da abin da ya faru da mutanen nan masu aljanu.
Et ceux qui les gardaient s'enfuirent; et étant venus dans la ville, ils racontèrent toutes ces choses, et ce qui était arrivé aux démoniaques.
34 Sai dukan garin suka fito don su taryi Yesu. Da suka kuwa gan shi, sai suka roƙe shi yă bar musu yanki.
Et voilà, toute la ville alla au-devant de Jésus, et l'ayant vu, ils le prièrent de se retirer de leur pays.

< Mattiyu 8 >