< Malaki 1 >

1 Annabci, wannan ita ce maganar Ubangiji ga Isra’ila ta wurin Malaki.
THE BURDEN of the word of the LORD to Israel by Malachi.
2 “Na ƙaunace ku, in ji Ubangiji. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya ka ƙaunace mu?’ “Isuwa ba ɗan’uwan Yaƙub ba ne?” In ji Ubangiji. “Duk da haka na ƙaunaci Yaƙub,
I have loved you, saith the LORD. Yet ye say: 'Wherein hast Thou loved us?' Was not Esau Jacob's brother? saith the LORD; yet I loved Jacob;
3 amma na ƙi Isuwa, na kuma mai da ƙasarsa da take kan duwatsu kango, na ba da gādonsa ga dilolin hamada.”
But Esau I hated, and made his mountains a desolation, and gave his heritage to the jackals of the wilderness.
4 Edom zai iya cewa, “Ko da yake an ragargaza mu, ai, za mu sāke gina kufanmu.” Amma ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Za su iya gini, amma zan rushe. Za a ce da su Muguwar Ƙasa, mutane da kullum suke a ƙarƙashi fushin Ubangiji.
Whereas Edom saith: 'We are beaten down, but we will return and build the waste places'; thus saith the LORD of hosts: They shall build, but I will throw down; and they shall be called The border of wickedness, and The people whom the LORD execrateth for ever.
5 Za ku ga wannan da idanunku ku kuma ce, ‘Ubangiji da girma yake, har gaba da iyakokin Isra’ila ma!’
And your eyes shall see, and ye shall say: 'The LORD is great beyond the border of Israel.'
6 “Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bawa kuma yakan girmama maigidansa. In ni mahaifi ne, ina girman da ya dace da ni? In ni maigida ne, ina girman da ya dace da ni?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Ku firistoci, ku ne kuka rena sunana. “Amma sai kuka ce, ‘Yaya muka rena sunanka?’
A son honoureth his father, and a servant his master; if then I be a father, where is My honour? and if I be a master, where is My fear? saith the LORD of hosts unto you, O priests, that despise My name. And ye say: 'Wherein have we despised Thy name?'
7 “Kun ajiye abinci mai ƙazanta a kan bagadena. “Sai kuka ce, ‘Yaya muka ƙazantar da kai?’ “Ta wurin cewa teburin Ubangiji abin reni ne.
Ye offer polluted bread upon Mine altar. And ye say: 'Wherein have we polluted thee?' In that ye say: 'The table of the LORD is contemptible.'
8 Sa’ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, wannan daidai ne? Sa’ad da kuka miƙa gurguwar dabba ko marar lafiya, wannan daidai ne? Ku gwada ba wa gwamnanku irin wannan ku gani! Kuna gani zai ji daɗinku? Zai karɓe ku ne?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
And when ye offer the blind for sacrifice, is it no evil! And when ye offer the lame and sick, is it no evil! Present it now unto thy governor; will he be pleased with thee? or will he accept thy person? saith the LORD of hosts.
9 “To, firistoci yanzu ku gwada ku roƙi Allah yă yi mana alheri. Da irin hadayun nan a hannuwanku ne zai ji ku?” In ji Ubangiji Maɗaukaki.
And now, I pray you, entreat the favour of God that He may be gracious unto us! — This hath been of your doing. — Will He accept any of your persons? saith the LORD of hosts.
10 “Kash, da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ba na jin daɗinku, ba zan kuwa karɓi hadaya daga hannuwanku ba” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Oh that there were even one among you that would shut the doors, that ye might not kindle fire on Mine altar in vain! I have no pleasure in you, saith the LORD of hosts, neither will I accept an offering at your hand.
11 Sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, daga fitowar rana har zuwa fāɗuwarta. A kowane wuri za a miƙa wa sunana turare da tsabtacciyar hadaya domin sunana zai zama mai girma a cikin al’ummai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
For from the rising of the sun even unto the going down of the same My name is great among the nations; and in every place offerings are presented unto My name, even pure oblations; for My name is great among the nations, saith the LORD of hosts.
12 “Amma kun ƙazantar da sunana ta wurin cewa ‘Teburin Ubangiji ya ƙazantu,’ kuka kuma yi magana a kan abincinsa kuna cewa, ‘Abin reni ne.’
But ye profane it, in that ye say: 'The table of the LORD is polluted, and the fruit thereof, even the food thereof, is contemptible.'
13 Kun kuma ce, ‘Mun gaji da irin wannan wahala!’ Kuna hura mini hancin reni,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Sa’ad da kuka kawo raunannu, gurguntattun dabbobi, ko kuma dabbobi masu fama da cuta, kuka kuma miƙa su hadaya, kuna gani zan karɓi wannan daga gare ku?” In ji Ubangiji.
Ye say also: 'Behold, what a weariness is it!' and ye have snuffed at it, saith the LORD of hosts; and ye have brought that which was taken by violence, and the lame, and the sick; thus ye bring the offering; should I accept this of your hand? saith the LORD.
14 “La’ananne ne macucin da yake da lafiyayyiyar dabba namiji a garkensa wadda ya yi alkawari zai bayar, amma sai ya miƙa hadayar dabba mai aibi ga Ubangiji. Gama ni babban sarki ne, za a kuma ji tsoron sunana a cikin al’ummai,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
But cursed be he that dealeth craftily, whereas he hath in his flock a male, and voweth, and sacrificeth unto the Lord a blemished thing; for I am a great King, saith the LORD of hosts, and My name is feared among the nations.

< Malaki 1 >