< Firistoci 9 >
1 A rana ta takwas, Musa ya kira Haruna da’ya’yansa maza da kuma dattawan Isra’ila.
A u osmi dan sazva Mojsije Arona i sinove njegove i starješine Izrailjske.
2 Ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki ɗan maraƙi domin hadayarka don zunubi da kuma ɗan rago domin hadaya ta ƙonawa, dukan biyu su kasance marar lahani, ka miƙa su a gaban Ubangiji.
I reèe Aronu: uzmi tele za žrtvu radi grijeha i ovna za žrtvu paljenicu, oba zdrava; i prinesi ih pred Gospodom.
3 Sa’an nan ka ce wa Isra’ilawa, ‘Ku ɗauki bunsuru na yin hadaya don zunubi, da ɗan maraƙi bana ɗaya, da ɗan rago bana ɗaya marasa lahani, don hadaya ta ƙonawa,
A sinovima Izrailjevim kaži i reci: uzmite jare za žrtvu radi grijeha, i tele i jagnje, oboje od godine dana, i zdravo, za žrtvu paljenicu.
4 da bijimi da rago don hadayun salama, a yi hadaya da su ga Ubangiji, da hadaya ta gari da aka kwaɓa da mai, gama yau Ubangiji zai bayyana a gare ku.’”
I vola i ovna za žrtvu zahvalnu, da prinesete pred Gospodom, i dar s uljem zamiješen, jer æe vam se danas javiti Gospod.
5 Suka ɗauki abubuwan da Musa ya umarta zuwa gaban Tentin Sujada, sai dukan jama’a suka zo kusa suka tsaya a gaban Ubangiji.
I uzeše što zapovjedi Mojsije, i donesoše pred šator od sastanka, i pristupivši sav zbor stadoše pred Gospodom.
6 Sa’an nan Musa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya umarce ku ku yi, domin ɗaukakar Ubangiji za tă bayyana gare ku.”
I reèe Mojsije: uèinite što je zapovjedio Gospod, i pokazaæe vam se slava Gospodnja.
7 Musa ya ce wa Haruna, “Matsa kusa da bagaden, ka miƙa hadayarka don zunubi, da hadayarka ta ƙonawa, ka yi kafara don kanka da kuma don jama’a. Ka kuma kawo hadayar jama’a, ka yi kafara dominsu kamar yadda Ubangiji ya umarta.”
I reèe Mojsije Aronu: pristupi k oltaru, i prinesi žrtvu za grijeh svoj i žrtvu svoju paljenicu, i oèisti od grijeha sebe i narod; i prinesi žrtvu narodu i oèisti ih od grijeha, kao što je zapovjedio Gospod.
8 Sai Haruna ya matsa kusa da bagaden, ya yanka ɗan maraƙi na yin hadaya don zunubi saboda kansa.
Tada Aron pristupi k oltaru, i zakla tele za se.
9 ’Ya’yan Haruna maza suka kawo masa jinin, ya kuma tsoma yatsarsa a cikin jinin ya zuba cikin ƙahonin bagade; sauran jinin kuwa ya zuba a gindin bagaden.
I sinovi Aronovi dodaše mu krv, a on zamoèi prst svoj u krv, i pomaza rogove oltaru; a ostalu krv izli na podnožje oltaru.
10 A kan bagaden, ya ƙone kitsen, ƙodojin, da abin da ya rufe hanta, daga hadaya don zunubi, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
A salo i bubrege i mrežicu s jetre od žrtve za grijeh zapali na oltaru, kao što bješe zapovjedio Gospod Mojsiju.
11 Naman da fatar kuwa ya ƙone waje da sansanin.
A meso i kožu sažeže ognjem iza okola.
12 Sa’an nan ya yanka hadaya ta ƙonawa.’Ya’yan Haruna maza suka miƙa masa jinin, ya kuwa yayyafa shi a kowane gefe na bagaden.
Potom zakla žrtvu svoju paljenicu, i sinovi Aronovi dodaše mu krv od nje, i pokropi njom oltar ozgo unaokolo.
13 Suka miƙa masa hadaya ta ƙonawa gunduwa-gunduwa, haɗe da kan, ya kuwa ƙone su a bisa bagaden.
I dodaše mu žrtvu paljenicu isjeèenu na dijelove zajedno s glavom, i zapali je na oltaru.
14 Sai ya wanke kayan ciki da ƙafafun, ya kuwa ƙone su tare da hadaya ta ƙonawa a kan bagade.
I opravši crijeva i noge od nje, zapali ih na oltaru svrh žrtve paljenice.
15 Sa’an nan Haruna ya kawo hadayar da take domin mutane. Ya ɗauki akuya ta hadaya don zunubin mutane, ya yanka shi, ya miƙa shi domin hadaya don zunubi kamar yadda ya yi da na farko.
Potom prinese žrtvu narodnu: uze jare za grijeh koje bješe za narod, i zakla ga, i prinese za grijeh kao i prvo.
16 Ya kawo hadaya ta ƙonawa ya kuma miƙa ta yadda aka tsara.
Iza toga prinese i žrtvu paljenicu, i svrši po zakonu.
17 Ya kuma kawo hadaya ta gari, ya ɗiba a tafi hannu ya ƙone a kan bagade tare da hadaya ta ƙonawa ta safe.
Prinese i dar, i uzevši od njega punu šaku zapali na oltaru svrh jutrenje žrtve paljenice.
18 Haruna ya yanka maraƙin da ragon a matsayin hadaya ta salama domin mutane.’Ya’yansa maza suka miƙa masa jinin, ya kuwa yayyafa shi a kowane gefe na bagade.
Potom zakla vola i ovna na žrtvu zahvalnu za narod; i dodaše mu sinovi Aronovi krv, i pokropi njom oltar ozgo unaokolo.
19 Amma sashen kitsen maraƙin da na ragon, da wutsiya mai kitse, da kitsen da yake rufe da kayan ciki, da ƙodoji da kuma kitsen da ya rufe hanta,
Pa mu dodaše i salo od vola, i od ovna rep, i salo što pokriva crijeva, i bubrege i mrežicu s jetre,
20 suka shimfiɗa waɗannan a kan ƙirjin, sa’an nan Haruna ya ƙone kitsen a kan bagade.
I metnuše sve salo na grudi, i zapali salo na oltaru.
21 Sai Haruna ya kaɗa ƙirjin da kuma cinyar dama a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa, kamar yadda Musa ya umarta.
A grudi i desno pleæe obrnu Aron tamo i amo na žrtvu obrtanu pred Gospodom, kao što bješe Gospod zapovjedio Mojsiju.
22 Sa’an nan Haruna ya ɗaga hannuwansa wajen mutane ya sa musu albarka. Da yake ya miƙa hadaya don zunubi, hadaya ta ƙonawa da kuma hadaya ta salama, sai ya sauka.
Tada podiže Aron ruke svoje prema narodu i blagoslovi ih; i siðe svršiv žrtvu za grijeh i žrtvu paljenicu i žrtvu zahvalnu.
23 Sai Musa da Haruna suka shiga cikin Tentin Sujada. Da suka fita, sai suka sa wa mutane albarka; sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan mutane.
Potom uðe Mojsije s Aronom u šator od sastanka, a kad opet izaðoše blagosloviše narod; i slava se Gospodnja pokaza svemu narodu.
24 Sai wuta ta fito daga gaban Ubangiji ta cinye hadaya ta ƙonawa da sassan kitsen a kan bagaden. Sa’ad da dukan mutane suka ga haka, sai suka yi ihu suna farin ciki, suka fāɗi rubda ciki, suka yi sujada.
Jer doðe oganj od Gospoda, i spali na oltaru žrtvu paljenicu i salo. I vidjevši to sav narod povika i pade nièice.