< Firistoci 16 >

1 Ubangiji ya yi magana da Musa bayan mutuwar’ya’yan Haruna biyu maza waɗanda suka mutu sa’ad da suka kusaci Ubangiji.
And YHWH speaks to Moses after the death of the two sons of Aaron, in their drawing near before YHWH, and they die;
2 Ubangiji ya ce wa Musa, “Faɗa wa ɗan’uwanka Haruna, kada yă riƙa shiga Wuri Mafi Tsarki bayan labule koyaushe, wato, a gaban murfi wanda yake bisa akwatin alkawari, domin kada yă mutu, gama zan bayyana a cikin girgije a kan murfin.
indeed, YHWH says to Moses, “Speak to your brother Aaron, and he does not come in at all times to the holy place within the veil, to the front of the propitiatory covering, which [is] on the Ark, and he does not die, for I am seen in a cloud on the propitiatory covering.
3 “Ga yadda Haruna zai shiga wuri mai tsarki, zai zo da ɗan bijimi domin hadaya don zunubi da kuma rago domin hadaya ta ƙonawa.
With this Aaron comes into the holy place: with a bullock, a son of the herd, for a sin-offering, and a ram for a burnt-offering;
4 Zai sa toguwar lilin mai tsarki, tare da ɗan ciki na lilin; zai yi ɗamara da igiya kewaye da shi, yă kuma sa hular lilin. Waɗannan su ne riguna masu tsarki; saboda haka dole yă yi wanka kafin yă sa su.
he puts on a holy linen coat, and linen trousers are on his flesh, and he girds himself with a linen girdle, and he wraps himself up with a linen turban; they [are] holy garments; and he has bathed his flesh with water and put them on.
5 Zai ɗauki bunsurai biyu daga jama’ar Isra’ilawa na hadaya don zunubi da ɗan rago don hadaya ta ƙonawa.
And from the congregation of the sons of Israel he takes two kids of the goats for a sin-offering and one ram for a burnt-offering;
6 “Haruna zai miƙa bijimi hadaya don zunubinsa yă kuma yi kafara don kansa da gidansa.
and Aaron has brought the bullock of the sin-offering near, which is his own, and has made atonement for himself and for his house;
7 Sa’an nan zai ɗauki bunsurai biyu yă miƙa su a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada.
and he has taken the two goats, and has caused them to stand before YHWH, at the opening of the Tent of Meeting.
8 Haruna zai jefa ƙuri’a don awaki biyun ɗin, ƙuri’a ɗaya domin Ubangiji, ɗayan kuma don azazel
And Aaron has given lots over the two goats, one lot for YHWH and one lot for a goat of departure;
9 Haruna zai kawo akuyar da ƙuri’a ta fāɗi a kai wa Ubangiji yă miƙa ta na hadaya don zunubi.
and Aaron has brought the goat near, on which the lot for YHWH has gone up, and has made it a sin-offering.
10 Amma za a miƙa akuyar da aka zaɓa ta wurin ƙuri’a a matsayi ta azazel da rai a gaban Ubangiji don a yi amfani da ita don kafara ta wurin korinta zuwa cikin jeji kamar azazel.
And the goat on which the lot for a goat of departure has gone up is caused to stand living before YHWH to make atonement by it, to send it away for a goat of departure into the wilderness.
11 “Haruna zai kawo bijimi domin hadayarsa ta zunubi don yă yi kafara wa kansa da kuma domin gidansa, zai kuma yanka bijimin domin nasa hadaya don zunubi.
And Aaron has brought the bullock of the sin-offering near, which is his own, and has made atonement for himself and for his house, and has slaughtered the bullock of the sin-offering which [is] his own,
12 Zai ɗauki faranti cike da garwashin wuta daga bagade a gaban Ubangiji, yă kuma cika hannunsa biyu da turare mai ƙanshin da aka niƙa yă kai su bayan labule.
and has taken the fullness of the censer of burning coals of fire from off the altar, from before YHWH, and the fullness of his hands of thin spice-incense, and has brought [it] within the veil;
13 Zai sa turaren a wuta a gaban Ubangiji, hayaƙin turaren kuwa zai rufe murfin kafarar a bisa Akwatin Alkawari, don kada yă mutu.
and he has put the incense on the fire before YHWH, and the cloud of the incense has covered the propitiatory covering which [is] on the Testimony, and he does not die.
14 Zai ɗibi jinin bijimin da yatsarsa yă yayyafa a gaban murfin kafarar; sa’an nan yă yayyafa jinin da yatsarsa sau bakwai a gaban murfin kafarar.
And he has taken of the blood of the bullock, and has sprinkled with his finger on the front of the propitiatory covering eastward; even at the front of the propitiatory covering he sprinkles seven times of the blood with his finger.
15 “Sa’an nan zai yanka akuya na hadaya don zunubi saboda mutane, yă kai jinin bayan labule, yă yi da shi yadda ya yi da jinin bijimin. Zai yayyafa shi a kan murfin kafarar da kuma a gabansa.
And he has slaughtered the goat of the sin-offering which [is] the people’s, and has brought in its blood to the inside of the veil, and has done with its blood as he has done with the blood of the bullock, and has sprinkled it on the propitiatory covering, and at the front of the propitiatory covering,
16 Ta haka zai yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki saboda ƙazantar tawayen Isra’ilawa, da laifofinsu, da dukan zunubansu. Haka zai yi saboda Tentin Sujada wanda yake a cikinsu a tsakiyar ƙazantarsu.
and he has made atonement for the holy place because of the uncleanness of the sons of Israel, and because of their transgressions in all their sins; and so he does for the Tent of Meeting which is dwelling with them in the midst of their uncleannesses.
17 Kada kowa yă kasance a Tentin Sujada daga lokacin da Haruna ya shiga don yă yi kafara a Wuri Mafi Tsarki har sai ya fita, bayan ya yi kafara domin kansa, gidansa da kuma dukan jama’ar Isra’ila.
And no man is in the Tent of Meeting in his going in to make atonement in the holy place, until his coming out; and he has made atonement for himself, and for his house, and for all the assembly of Israel.
18 “Sa’an nan zai fita zuwa bagade da yake a gaban Ubangiji, yă yi kafara dominsa. Zai ɗibi jinin bijimi da na akuya yă zuba a ƙahonin bagade.
And he has gone out to the altar which [is] before YHWH, and has made atonement for it; and he has taken of the blood of the bullock and of the blood of the goat, and has put [it] around the horns of the altar;
19 Zai yayyafa jinin a kan bagade da yatsarsa sau bakwai, yă tsabtacce shi yă kuma tsarkake shi daga ƙazantar Isra’ilawa.
and he has sprinkled on it of the blood with his finger seven times, and has cleansed it, and has hallowed it from the uncleannesses of the sons of Israel.
20 “Sa’ad da Haruna ya gama yin kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da kuma bagade, sai yă kawo akuya mai rai.
And he has ceased from making atonement [for] the holy place, and the Tent of Meeting, and the altar, and has brought the living goat near;
21 Haruna zai ɗibiya hannuwansa a kan akuya mai ran, yă furta a kansa dukan mugunta da tawayen Isra’ilawa, dukan zunubansu, yă kuma sa su a kan akuyan. Zai kori akuyan zuwa cikin jeji a hannun mutumin da aka ba shi aikin yin haka.
and Aaron has laid his two hands on the head of the living goat, and has confessed over it all the iniquities of the sons of Israel, and all their transgressions in all their sins, and has put them on the head of the goat, and has sent [it] away by the hand of a ready man into the wilderness;
22 Akuyan zai ɗauka a kansa dukan zunubansu zuwa kaɗaitaccen wuri, a can mutumin zai sake shi a jeji.
and the goat has borne on himself all their iniquities to a land of separation. And he has sent the goat away into the wilderness,
23 “Sa’an nan Haruna zai shiga Tentin Sujada yă tuɓe rigunansa na lilin da ya sa, kafin yă shiga Wuri Mafi Tsarki, zai kuma bar su a can.
and Aaron has come into the Tent of Meeting, and has stripped off the linen garments which he had put on in his going into the holy place, and has placed them there;
24 Zai yi wanka a tsattsarkan wuri yă sa rigunarsa na kullum. Sa’an nan zai fita yă miƙa hadaya ta ƙonawa domin kansa da hadaya ta ƙonawa domin mutane, don yă yi kafara domin kansa da kuma domin mutane.
and he has bathed his flesh with water in the holy place, and has put on his garments, and has come out, and has made his burnt-offering, and the burnt-offering of the people, and has made atonement for himself and for the people;
25 Zai kuma ƙone kitsen hadaya don zunubi a kan bagade.
and with the fat of the sin-offering he makes incense on the altar.
26 “Dole mutumin da ya saki akuya na azazel yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka; bayan haka zai iya shiga sansani.
And he who is sending the goat away for a goat of departure washes his garments, and has bathed his flesh with water, and afterward he comes into the camp.
27 Dole a ɗauki jini, fata, nama da kuma ƙashin bijimi da akuyan hadaya don zunubi, waɗanda aka kawo jininsu cikin Wuri Mafi Tsarki don kafara, a kai waje da sansani a ƙone.
And the bullock of the sin-offering and the goat of the sin-offering, whose blood has been brought in to make atonement in the holy place, [one] brings out to the outside of the camp, and they have burned their skins, and their flesh, and their dung with fire;
28 Dole mutumin da ya ƙone su yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka, bayan haka zai iya shiga sansani.
and he who is burning them washes his garments, and has bathed his flesh with water, and afterward he comes into the camp.
29 “Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare ku. A rana ta goma ga wata na bakwai, dole ku yi mūsu kanku, ba kuwa za ku yi wani aiki ba, ko da mutum baƙo ne a cikinku ko kuwa ɗan ƙasa,
And it has been for a continuous statute to you, in the seventh month, on the tenth of the month, you humble yourselves, and do no work—the native and the sojourner who is sojourning in your midst;
30 gama a wannan rana za a yi kafara dominku, don a tsarkake ku. Sa’an nan a gaban Ubangiji, za a tsarkake ku daga dukan zunubanku.
for on this day he makes atonement for you, to cleanse you; you are clean from all your sins before YHWH;
31 Asabbaci ne don hutawa, kuma dole ku yi mūsun kanku; wannan dawwammamiyar farilla ce.
it [is] a Sabbath of rest for you, and you have humbled yourselves—a continuous statute.
32 Firist da aka keɓe aka kuma naɗa don yă gāji mahaifinsa a matsayin babban firist ne zai yi kafara. Zai sa rigunan lilin masu tsarki
And the priest whom he anoints, and whose hand he consecrates to act as priest instead of his father, has made atonement, and has put on the linen garments, the holy garments;
33 yă yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da bagade, da kuma saboda firistoci da kuma dukan jama’ar Isra’ila.
and he has made atonement [for] the holy sanctuary; and [for] the Tent of Meeting, even [for] the altar he makes atonement; indeed, he makes atonement for the priests and for all the people of the assembly.
34 “Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce gare ku. Za a riƙa yin kafara sau ɗaya a shekara saboda dukan zunuban Isra’ilawa.” Aka kuma yi haka, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And this has been for a continuous statute to you, to make atonement for the sons of Israel, because of all their sins, once in a year”; and he does as YHWH has commanded Moses.

< Firistoci 16 >