< Firistoci 16 >
1 Ubangiji ya yi magana da Musa bayan mutuwar’ya’yan Haruna biyu maza waɗanda suka mutu sa’ad da suka kusaci Ubangiji.
Fvrthermore the Lord spake vnto Moses, after the death of the two sonnes of Aaron, whe they came to offer before the Lord, and dyed:
2 Ubangiji ya ce wa Musa, “Faɗa wa ɗan’uwanka Haruna, kada yă riƙa shiga Wuri Mafi Tsarki bayan labule koyaushe, wato, a gaban murfi wanda yake bisa akwatin alkawari, domin kada yă mutu, gama zan bayyana a cikin girgije a kan murfin.
And the Lord sayd vnto Moses, Speake vnto Aaron thy brother, that he come not at all times into the Holy place within the vayle, before the Merciseate, which is vpon the Arke, that he dye not: for I wil appeare in the cloude vpon the Merciseate.
3 “Ga yadda Haruna zai shiga wuri mai tsarki, zai zo da ɗan bijimi domin hadaya don zunubi da kuma rago domin hadaya ta ƙonawa.
After this sort shall Aaron come into the Holy place: euen with a yong bullocke for a sinne offring, and a ramme for a burnt offring.
4 Zai sa toguwar lilin mai tsarki, tare da ɗan ciki na lilin; zai yi ɗamara da igiya kewaye da shi, yă kuma sa hular lilin. Waɗannan su ne riguna masu tsarki; saboda haka dole yă yi wanka kafin yă sa su.
He shall put on the holy linnen coate, and shall haue linnen breeches vpon his flesh, and shall be girded with a linnen girdle, and shall couer his head with a linnen miter: these are the holy garments: therefore shall hee wash his flesh in water, when he doeth put them on.
5 Zai ɗauki bunsurai biyu daga jama’ar Isra’ilawa na hadaya don zunubi da ɗan rago don hadaya ta ƙonawa.
And hee shall take of the Congregation of the children of Israel, two hee goates for a sinne offring, and a ramme for a burnt offring.
6 “Haruna zai miƙa bijimi hadaya don zunubinsa yă kuma yi kafara don kansa da gidansa.
Then Aaron shall offer the bullocke for his sinne offring, and make an atonement for himselfe, and for his house.
7 Sa’an nan zai ɗauki bunsurai biyu yă miƙa su a gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada.
And he shall take the two hee goates, and present them before the Lord at the doore of the Tabernacle of the Congregation.
8 Haruna zai jefa ƙuri’a don awaki biyun ɗin, ƙuri’a ɗaya domin Ubangiji, ɗayan kuma don azazel
Then Aaron shall cast lots ouer the two hee goates: one lot for the Lord, and the other for the Scape goate.
9 Haruna zai kawo akuyar da ƙuri’a ta fāɗi a kai wa Ubangiji yă miƙa ta na hadaya don zunubi.
And Aaron shall offer the goat, vpon which the Lords lot shall fal, and make him a sinne offring.
10 Amma za a miƙa akuyar da aka zaɓa ta wurin ƙuri’a a matsayi ta azazel da rai a gaban Ubangiji don a yi amfani da ita don kafara ta wurin korinta zuwa cikin jeji kamar azazel.
But the goate, on which the lot shall fall to be the Scape goate, shalbe presented aliue before the Lord, to make reconciliation by him, and to let him go (as a Scape goate) into the wildernes.
11 “Haruna zai kawo bijimi domin hadayarsa ta zunubi don yă yi kafara wa kansa da kuma domin gidansa, zai kuma yanka bijimin domin nasa hadaya don zunubi.
Thus Aaron shall offer the bullocke for his sinne offring, and make a reconciliation for himselfe, and for his house, and shall kill the bullocke for his sinne offring.
12 Zai ɗauki faranti cike da garwashin wuta daga bagade a gaban Ubangiji, yă kuma cika hannunsa biyu da turare mai ƙanshin da aka niƙa yă kai su bayan labule.
And he shall take a censer full of burning coles from off the altar before the Lord, and his handfull of sweete incense beaten small, and bring it within the vayle,
13 Zai sa turaren a wuta a gaban Ubangiji, hayaƙin turaren kuwa zai rufe murfin kafarar a bisa Akwatin Alkawari, don kada yă mutu.
And shall put the incense vpon the fire before the Lord, that the cloude of the incense may couer the Merciseat that is vpon the Testimonie: so he shall not dye.
14 Zai ɗibi jinin bijimin da yatsarsa yă yayyafa a gaban murfin kafarar; sa’an nan yă yayyafa jinin da yatsarsa sau bakwai a gaban murfin kafarar.
And hee shall take of the blood of the bullocke, and sprinkle it with his finger vpon the Merciseat Eastward: and before the Merciseate shall he sprinkle of the blood with his finger seuen times.
15 “Sa’an nan zai yanka akuya na hadaya don zunubi saboda mutane, yă kai jinin bayan labule, yă yi da shi yadda ya yi da jinin bijimin. Zai yayyafa shi a kan murfin kafarar da kuma a gabansa.
Then shall he kill the goate that is the peoples sinne offring, and bring his blood within the vaile, and doe with that blood, as he did with the blood of the bullocke, and sprinckle it vpon the Merciseate, and before the Merciseate.
16 Ta haka zai yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki saboda ƙazantar tawayen Isra’ilawa, da laifofinsu, da dukan zunubansu. Haka zai yi saboda Tentin Sujada wanda yake a cikinsu a tsakiyar ƙazantarsu.
So he shall purge the Holy place from the vncleannes of the children of Israel, and from their trespasses of all their sinnes: so shall he do also for the Tabernacle of the Cogregation placed with them, in the middes of their vncleannesse.
17 Kada kowa yă kasance a Tentin Sujada daga lokacin da Haruna ya shiga don yă yi kafara a Wuri Mafi Tsarki har sai ya fita, bayan ya yi kafara domin kansa, gidansa da kuma dukan jama’ar Isra’ila.
And there shalbe no man in the Tabernacle of the Congregation, when he goeth in to make an atonement in the Holy place, vntill hee come out, and haue made an atonement for himselfe, and for his housholde, and for all the Congregation of Israel.
18 “Sa’an nan zai fita zuwa bagade da yake a gaban Ubangiji, yă yi kafara dominsa. Zai ɗibi jinin bijimi da na akuya yă zuba a ƙahonin bagade.
After, he shall goe out vnto the altar that is before the Lord and make a reconciliation vpon it, and shall take of the blood of the bullocke, and of the blood of the goate, and put it vpon the hornes of the Altar round about:
19 Zai yayyafa jinin a kan bagade da yatsarsa sau bakwai, yă tsabtacce shi yă kuma tsarkake shi daga ƙazantar Isra’ilawa.
So shall hee sprinkle of the blood vpon it with his finger seuen times, and clense it, and halowe it from the vncleannes of the children of Israel.
20 “Sa’ad da Haruna ya gama yin kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da kuma bagade, sai yă kawo akuya mai rai.
When he hath made an ende of purging the Holy place, and the Tabernacle of the Congregation, and the altar, then he shall bring the liue goate:
21 Haruna zai ɗibiya hannuwansa a kan akuya mai ran, yă furta a kansa dukan mugunta da tawayen Isra’ilawa, dukan zunubansu, yă kuma sa su a kan akuyan. Zai kori akuyan zuwa cikin jeji a hannun mutumin da aka ba shi aikin yin haka.
And Aaron shall put both his handes vpon the head of the liue goate, and confesse ouer him al the iniquities of the children of Israel, and all their trespasses, in all their sinnes, putting them vpon the head of the goate, and shall sende him away (by the hand of a man appointed) into the wildernes.
22 Akuyan zai ɗauka a kansa dukan zunubansu zuwa kaɗaitaccen wuri, a can mutumin zai sake shi a jeji.
So the goate shall beare vpon him all their iniquities into the land that is not inhabited, and he shall let the goate go into the wildernesse.
23 “Sa’an nan Haruna zai shiga Tentin Sujada yă tuɓe rigunansa na lilin da ya sa, kafin yă shiga Wuri Mafi Tsarki, zai kuma bar su a can.
After, Aaron shall come into the Tabernacle of the Congregation, and put off the linnen clothes, which he put on when he went into the Holy place, and leaue them there.
24 Zai yi wanka a tsattsarkan wuri yă sa rigunarsa na kullum. Sa’an nan zai fita yă miƙa hadaya ta ƙonawa domin kansa da hadaya ta ƙonawa domin mutane, don yă yi kafara domin kansa da kuma domin mutane.
Hee shall wash also his flesh with water in the Holy place, and put on his owne rayment, and come out, and make his burnt offring, and the burnt offring of the people, and make an atonement for himselfe, and for the people.
25 Zai kuma ƙone kitsen hadaya don zunubi a kan bagade.
Also the fatte of the sinne offring shall he burne vpon the altar.
26 “Dole mutumin da ya saki akuya na azazel yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka; bayan haka zai iya shiga sansani.
And he that caried forth the goat, called the Scape goat, shall wash his clothes, and wash his flesh in water, and after that shall come into the hoste.
27 Dole a ɗauki jini, fata, nama da kuma ƙashin bijimi da akuyan hadaya don zunubi, waɗanda aka kawo jininsu cikin Wuri Mafi Tsarki don kafara, a kai waje da sansani a ƙone.
Also the bullocke for the sinne offring, and the goate for the sinne offring (whose blood was brought to make a reconciliation in the Holy place) shall one carie out without the hoste to be burnt in the fire, with their skinnes, and with their flesh, and with their doung.
28 Dole mutumin da ya ƙone su yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka, bayan haka zai iya shiga sansani.
And hee that burneth them shall wash his clothes, and wash his flesh in water, and afterward come into the hoste.
29 “Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla a gare ku. A rana ta goma ga wata na bakwai, dole ku yi mūsu kanku, ba kuwa za ku yi wani aiki ba, ko da mutum baƙo ne a cikinku ko kuwa ɗan ƙasa,
So this shalbe an ordinance for euer vnto you: the tenth day of the seuenth moneth, yee shall humble your soules, and do no worke at all, whether it be one of the same countrey or a strager that soiourneth among you.
30 gama a wannan rana za a yi kafara dominku, don a tsarkake ku. Sa’an nan a gaban Ubangiji, za a tsarkake ku daga dukan zunubanku.
For that day shall ye Priest make an atonement for you to clense you: ye shalbe cleane from all your sinnes before the Lord.
31 Asabbaci ne don hutawa, kuma dole ku yi mūsun kanku; wannan dawwammamiyar farilla ce.
This shall be a Sabbath of rest vnto you, and ye shall humble your soules, by an ordinance for euer.
32 Firist da aka keɓe aka kuma naɗa don yă gāji mahaifinsa a matsayin babban firist ne zai yi kafara. Zai sa rigunan lilin masu tsarki
And the Priest whom he shall anoynt, and whom he shall cosecrate (to minister in his fathers steade) shall make the atonement, and shall put on the linnen clothes and Holy vestments,
33 yă yi kafara domin Wuri Mafi Tsarki, Tentin Sujada da bagade, da kuma saboda firistoci da kuma dukan jama’ar Isra’ila.
And shall purge the Holy Sanctuarie and the Tabernacle of the Congregation, and shall clense the altar, and make an atonement for the Priests and for all the people of the Congregation.
34 “Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ce gare ku. Za a riƙa yin kafara sau ɗaya a shekara saboda dukan zunuban Isra’ilawa.” Aka kuma yi haka, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
And this shalbe an euerlasting ordinance vnto you, to make an atonement for the children of Israel for all their sinnes once a yeere: and as the Lord commanded Moses, he did.