< Firistoci 15 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
And the Lord said to Moses and to Aaron,
2 “Yi wa Isra’ilawa magana, ku ce musu, ‘Duk sa’ad da wani namiji yake ɗiga daga azzakarinsa, wannan ɗiga marar tsarki ne.
Say to the children of Israel: If a man has an unclean flow from his flesh, it will make him unclean.
3 Ko ɗigar ta ci gaba da fitowa daga azzakarinsa ko an tsere ta, za tă sa mutumin yă zama marar tsarki. Ga yadda ɗigarsa za tă kawo ƙazantuwa,
If the flow goes on or if the part is stopped up, to keep back the flow, he is still unclean.
4 “‘Duk gadon da mutumin mai ɗigar ya kwanta a kai, zai zama marar tsarki, kuma duk abin da ya zauna a kai, zai zama marar tsarki.
Every bed on which he has been resting will be unclean, and everything on which he has been seated will be unclean.
5 Duk wanda ya taɓa gadonsa dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuwa ƙazantu har yamma.
And anyone touching his bed is to have his clothing washed and his body bathed in water and be unclean till evening.
6 Duk wanda ya zauna a inda wannan mai ɗiga ya zauna a kai, dole yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka, zai kuwa ƙazantu har yamma.
And he who has been seated on anything on which the unclean man has been seated is to have his clothing washed and his body bathed in water and be unclean till evening.
7 “‘Duk wanda ya taɓa jikin mai ɗiga, dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma.
And anyone touching the flesh of the unclean man is to have his clothing washed and his body bathed in water and be unclean till evening.
8 “‘In mai ɗiga ya tofa miyau a kan wani wanda yake tsarkakakke, dole tsarkakakken nan yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma.
And if liquid from the mouth of the unclean man comes on to him who is clean, then he is to have his clothing washed and his body bathed in water and be unclean till evening.
9 “‘Kowane sirdi da mai ɗigar ya zauna a kai zai ƙazantu,
And any leather seat on a horse on which the unclean man has been seated will be unclean.
10 kuma duk wanda ya taɓa wani abu cikin abubuwan da suke a ƙarƙashin sirdin zai ƙazantu har yamma; duk wanda ya ɗauki abubuwan nan dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka, zai kuwa ƙazantu har yamma.
And anyone touching anything which was under him will be unclean till the evening; anyone taking up any of these things is to have his clothing washed and his body bathed in water and be unclean till evening.
11 “‘Duk wanda mai ɗiga ya taɓa ba tare da ya wanke hannuwansa da ruwa ba, dole yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma.
And anyone on whom the unclean man puts his hands, without washing them in water, is to have his clothing washed and his body bathed in water and be unclean till evening.
12 “‘Dole a farfashe tukunya lakar da mutumin ya taɓa, kuma dole a ɗauraye duk wani abin da aka yi da katako wanda ya taɓa da ruwa.
And any vessel of earth which has been touched by the unclean man will have to be broken and any vessel of wood washed.
13 “‘Sa’ad da aka tsabtacce mai ɗigar, zai ɗauki kwana bakwai don tsabtaccewarsa; dole yă wanke rigunansa, yă kuma yi wanka mai tsabta, zai kuwa zama tsarkakakke.
And when a man who has a flow from his body is made clean from it, he is to take seven days to make himself clean, washing his clothing and bathing his body in flowing water, and then he will be clean.
14 A rana ta takwas dole yă ɗauki kurciyoyi biyu ko tattabarai biyu, yă zo gaban Ubangiji a ƙofar Tentin Sujada, yă ba da su ga firist.
And on the eighth day he is to take two doves or two young pigeons and come before the Lord to the door of the Tent of meeting and give them to the priest:
15 Firist ɗin zai miƙa su, ɗaya domin hadaya don zunubi, ɗayan kuma domin hadaya ta ƙonawa. Ta haka zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mai ɗigar.
And they are to be offered by the priest, one for a sin-offering and one for a burned offering, and the priest will take away his sin before the Lord on account of his flow.
16 “‘Sa’ad da namiji ya ɗigar maniyyi, dole yă wanke jikinsa gaba ɗaya da ruwa, zai kuma ƙazantu har yamma.
And if a man's seed goes out from him, then all his body will have to be bathed in water and he will be unclean till evening.
17 Dole a wanke duk riga ko fatar da yake da maniyyin a kansa da ruwa, zai kuma ƙazantu har yamma.
And any clothing or skin on which the seed comes is to be washed with water and be unclean till evening.
18 Sa’ad da namiji ya kwana da mace ya kuwa zub da maniyyi, dole dukansu biyu su yi wanka, za su kuma ƙazantu har yamma.
And if a man has sex relations with a woman and his seed goes out from him, the two of them will have to be bathed in water and will be unclean till evening.
19 “‘Sa’ad mace take al’adarta ta ƙa’ida, rashin tsabtarta ta al’adar zai ɗauki kwana bakwai, kuma duk wanda ya taɓa ta, zai ƙazantu har yamma.
And if a woman has a flow of blood from her body, she will have to be kept separate for seven days, and anyone touching her will be unclean till evening.
20 “‘Duk abin da ta kwanta a kai a lokacin al’adarta zai ƙazantu, kuma duk abin da ta zauna a kai zai ƙazantu.
And everything on which she has been resting, while she is kept separate, will be unclean, and everything on which she has been seated will be unclean.
21 Duk wanda ya taɓa gadonta dole yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma.
And anyone touching her bed will have to have his clothing washed and his body bathed in water and be unclean till evening.
22 Duk wanda ya taɓa wani abin da ta zauna a kai, dole yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma.
And anyone touching anything on which she has been seated will have to have his clothing washed and his body bathed in water and be unclean till evening.
23 Ko gado ne, ko kuwa wani abin da ta zauna a kai, sa’ad da wani ya taɓa shi, zai ƙazantu har yamma.
Anyone touching anything on the bed or on the thing on which she has been seated, will be unclean till evening.
24 “‘In namiji ya kwana da ita, al’adarta kuwa ta taɓa shi, zai ƙazantu na kwana bakwai; duk kuma gadon da ya kwanta a kai, zai ƙazantu.
And if any man has sex relations with her so that her blood comes on him, he will be unclean for seven days and every bed on which he has been resting will be unclean.
25 “‘Idan mace tana ɗigar jini na tsawon kwanaki, ban da kwanakin ganin al’adarta, ko kuwa idan al’adarta ya wuce yawan kwanakin da ya kamata, to, za tă ƙazantu daidai kamar na kwanakin al’adar da ta saba yi. Wato, muddin tana cikin ɗiga, ta zama mai ƙazanta.
And if a woman has a flow of blood for a long time, not at the time when she generally has it, or if the flow goes on longer than the normal time, she will be unclean while the flow of blood goes on, as she is at other normal times.
26 Duk gadon da ta kwanta yayinda ta ci gaba da ɗiga zai zama marar tsarki, kamar yadda gadonta yake a lokacin al’adarta, kuma duk abin da ta zauna a kai zai zama marar tsarki, kamar yadda yake a lokacin al’adarta.
Every bed on which she has been resting will be unclean, as at the times when she normally has a flow of blood, and everything on which she has been seated will be unclean, in the same way.
27 Duk wanda ta taɓa su zai zama marar tsarki; dole yă wanke rigunansa yă kuma yi wanka, zai kuma ƙazantu har yamma.
And anyone touching these things will be unclean, and his clothing will have to be washed and his body bathed in water and he will be unclean till evening.
28 “‘Sa’ad da aka tsabtacce ta daga ɗigarta, dole tă ɗauki kwana bakwai, bayan haka za tă zama mai tsarki.
But when her flow of blood is stopped, after seven days she will be clean.
29 A rana ta takwas, dole tă ɗauki kurciyoyi biyu ko tattabari biyu ta kawo su ga firist a bakin ƙofar Tentin Sujada.
And on the eighth day let her get two doves or two young pigeons and take them to the priest to the door of the Tent of meeting,
30 Firist zai miƙa ɗaya saboda hadaya don zunubi, ɗayan kuma don hadaya ta ƙonawa. Ta haka zai yi kafara dominta a gaban Ubangiji saboda ƙazantar ɗigarta.
To be offered by the priest, one for a sin-offering and one for a burned offering; and the priest will take away her sin before the Lord on account of her unclean condition.
31 “‘Ta haka za ka tsarkake Isra’ilawa daga rashin tsarkinsu, domin kada su mutu saboda rashin tsarkinsu ta wurin ƙazantar da wurin zamana wanda yake tsakiyarsu.’”
In this way may the children of Israel be made free from all sorts of unclean conditions, so that death may not overtake them when they are unclean and when they make unclean my holy place which is among them.
32 Waɗannan su ne ƙa’idodi a kan wanda yake ɗiga, da wanda yake zubar da maniyyi,
This is the law for the man who has a flow from his body, or whose seed goes from him so that he is unclean;
33 ƙa’idodi ne kuma ga mace wadda take al’ada, ga namiji ko macen da take ɗiga, ga kuma namijin da ya kwana da mace marar tsarki.
And for her who has a flow of blood, and for any man or woman who has an unclean flow, and for him who has sex relations with a woman when she is unclean.

< Firistoci 15 >