< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Ten en mente, oh Señor, lo que nos ha llegado; toma nota y ve nuestra vergüenza.
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Nuestra herencia se entrega a los hombres extranjeros, nuestras casas a aquellos que no son nuestros compatriotas.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
Somos hijos sin padres, nuestras madres son como viudas.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
Pagamos dinero por un vaso de agua, obtenemos nuestra madera por un precio.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Nuestros atacantes están sobre nuestros cuellos; vencidos con cansancio, no tenemos descanso.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
Hemos dado nuestras manos a los egipcios y a los asirios para que podamos tener suficiente pan.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Nuestros padres fueron pecadores y están muertos; y el peso de su maldad está sobre nosotros.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Los siervos gobiernan sobre nosotros, y no hay nadie que nos libere de sus manos.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
Ponemos nuestras vidas en peligro para obtener nuestro pan, enfrentándonos a la espada del desierto.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Nuestra piel se calienta como un horno, debido a la fiebre que nos causa la necesidad de alimentos.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
Tomaron por la fuerza a las mujeres en Sión, a las vírgenes en las ciudades de Judá.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Los príncipes fueron colgados de las manos; los rostros de los ancianos no fueron honrados.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
Los jóvenes trituraban el grano y los niños caían bajo el peso de la leña.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
Los ancianos ya no están sentados en la puerta, y la música de los jóvenes ha llegado a su fin.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
El gozo de nuestros corazones ha terminado; Nuestro baile se transforma en dolor.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
La corona ha sido quitada de nuestra cabeza; el dolor es nuestro, porque somos pecadores.
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
Por esto nuestros corazones son débiles; por estas cosas nuestros ojos son oscuros;
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
Por la montaña de Sión que es una ruina; los chacales van y vienen.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
Tú, oh Señor, estás sentado como Rey para siempre; El asiento de tu poder es de generación en generación.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
¿Por qué te olvidarás de nosotros para siempre? ¿Por qué has estado alejado de nosotros durante tanto tiempo?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Haz que volvamos a ti, Señor, y volveremos; Renueva nuestros días como en el pasado.
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
Pero nos has rechazado por completo; Estás lleno de ira contra nosotros.

< Makoki 5 >