< Makoki 3 >
1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
Yo soy un hombre que vio aflicción en la vara de su enojo.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Guióme, y me llevó en tinieblas, mas no en luz.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
Ciertamente contra mí volvió, y revolvió su mano todo el día.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
Hizo envejecer mi carne y mi piel: quebrantó mis huesos.
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
Edificó contra mí, y cercó me de tóxico, y de trabajo.
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
Asentóme en oscuridades como los muertos para siempre.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
Cercóme de seto, y no saldré: agravó mis grillos.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
Aun cuando clamé, y di voces, cerró mi oración.
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
Cercó de seto mis caminos a piedra tajada: torció mis senderos.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
Oso que asecha fue para mí, león en escondrijos.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
Torció mis caminos, y despedazóme: tornóme asolado.
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
Su arco entesó, y púsome como blanco a la saeta.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
Hizo entrar en mis riñones la saetas de su aljaba.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
Fui escarnio a todo mi pueblo, canción de ellos todos los días.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
Hartóme de amarguras, embriagóme de ajenjos.
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
Quebróme los dientes con cascajo, cubrióme de ceniza.
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
Y mi alma se alejó de la paz, olvidéme del bien.
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
Y dije: Pereció mi fortaleza, y mi esperanza de Jehová.
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Acuérdate de mi aflicción, y de mi abatimiento, del ajenjo, y de la hiel.
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
Acordándose se acordará, porque mi alma es humillada en mí.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
Esto reduciré a mi corazón; por tanto esperaré.
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
Misericordias de Jehová son, que no somos consumidos; porque sus misericordias nunca desfallecieron.
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
Nuevas cada mañana: grande es tu fe.
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
Mi parte es Jehová, dijo mi alma: por tanto a él esperaré.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
Bueno es Jehová a los que en él esperan, al alma que le buscare.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
Bueno es esperar callando en la salud de Jehová.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
Bueno es al varón, si llevare el yugo desde su mocedad.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Asentarse ha solo, y callará; porque llevó sobre sí.
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Pondrá su boca en el polvo, si quizá habrá esperanza.
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Dará la mejilla al que le hiriere: hartarse ha de afrenta.
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
Porque el Señor no desechará para siempre.
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
Antes si afligiere, también se compadecerá según la multitud de sus misericordias.
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
Porque no aflige, ni congoja de su corazón a los hijos de los hombres.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
Para desmenuzar debajo de sus pies todos los encarcelados de la tierra;
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
Para hacer apartar el derecho del hombre delante de la presencia del Altísimo;
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
Para trastornar al hombre en su causa, el Señor no lo sabe.
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
¿Quién será pues aquel que diga, que vino algo que el Señor no mandó?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
¿De la boca del Altísimo no saldrá malo ni bueno?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
¿Por qué pues tiene dolor el hombre viviente, el hombre en su pecado?
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Escudriñemos nuestros caminos, y busquemos, y volvámonos a Jehová.
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Levantemos nuestros corazones con las manos a Dios en los cielos.
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
Nosotros habemos rebelado, y fuimos desleales: por tanto tú no perdonaste.
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
Tendiste la ira, y perseguístenos; mataste, no perdonaste.
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
Cubrístete de nube, porque no pasase la oración.
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Raedura y abominación nos tornaste en medio de los pueblos.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
Todos nuestros enemigos abrieron sobre nosotros su boca.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Temor, y lazo fue a nosotros, asolamiento, y quebrantamiento.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Ríos de aguas echan mis ojos por el quebrantamiento de la hija de mi pueblo.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Mis ojos destilan, y no cesan; porque no hay relajación,
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
Hasta que Jehová mire, y vea desde los cielos.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Mis ojos contristaron a mi alma por todas las hijas de mi ciudad.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Cazando me cazarón mis enemigos como a ave, sin porqué.
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
Ataron mi vida en mazmorra, y pusieron piedra sobre mí.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Aguas vinieron de avenida sobre mi cabeza: yo dije: Muerto soy.
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
Invoqué tu nombre, o! Jehová, desde la cárcel profunda.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Oíste mi voz: no escondas tu oído a mi clamor, para que yo respire.
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Acercástete el día que te invoqué: dijiste: No temas.
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Pleiteaste, Señor, la causa de mi alma, redimiste mi vida.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Tú has visto, o! Jehová, mi sin razón: pleitea mi causa.
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Tú has visto, toda su venganza, todos sus pensamientos contra mí.
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
Tu has oído la afrenta de ellos, o! Jehová, todos sus pensamientos contra mí:
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
Los dichos de los que se levantaron contra mí, y su pensamiento contra mí siempre.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Su sentarse, y su levantarse mira: yo soy su canción.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Págales paga, o! Jehová, según la obra de sus manos.
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
Dáles ansia de corazón, dáles tu maldición.
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Persíguelos en furor, y quebrántalos de debajo de los cielos, o! Jehová.