< Makoki 1 >

1 Yanzu birnin ya zama babu kowa a ciki, birnin da a dā yake cike da mutane! Yanzu birnin ya zama kamar gwauruwa, wadda a dā babba ce ita a cikin ƙasashe! Ita da take sarauniya a cikin larduna yanzu ta zama baiwa.
Jerusalem was [once] full of people, but now it is deserted. [Once] it was honored by people all over the world, but now it is [grieving/abandoned] like [SIM] a widow. [Once] it was [honored like] [MET] a princess [is honored] among the nations, but now [we who live here] have become slaves.
2 Tana yin kuka mai zafi da dare, hawaye na gangara a kan kumatunta. A cikin masoyanta duka babu wanda ya yi mata ta’aziyya. Duk abokanta sun yashe ta; sun zama abokan gābanta.
We [PRS] weep bitterly [all] night long, with tears flowing down our cheeks. Among [the people in] all [the nations] that loved Jerusalem there are none that comfort us [now]. All [the rulers of those nations that were previously] our allies have betrayed us, and they are all now enemies [of the people of Jerusalem].
3 Bayan wahala da baƙin ciki, Yahuda ta tafi bauta. Ta zauna a cikin ƙasashe, ba tă samu wurin hutawa ba. Duk masu fafararta sun same ta sa’ad da take cikin matuƙar ɓacin rai.
[The people of] Judah have been (exiled/forced to go to other countries) and caused to suffer greatly as slaves. They live in [other] nations where they do not have peace/safety. Their enemies seized them, and there was no way for them to escape.
4 Hanyoyin zuwa Sihiyona suna makoki, gama ba wanda ya zo bikin da ta shirya. Ba kowa a hanyoyin shiganta. Firistocinta suna gurnani,’yan matana kuma suna wahala, kuma tana cikin shan wahala ƙwarai.
The roads to Zion [Hill] are empty [PRS] because no one comes [here] to [celebrate] the sacred festivals. The city gates are deserted, and the priests groan. The young women [of Jerusalem] cry [because] they are suffering greatly.
5 Maƙiyanta sun zama shugabanninta; Abokan gābanta suna da kwanciyar rai. Ubangiji ya kawo mata ɓacin rai domin yawan zunubanta.’Ya’yanta sun tafi bauta, a ƙarƙashin maƙiyanta.
Our enemies have conquered the city, and [now] they prosper. Yahweh has punished [the people of] Jerusalem because of all the sins that they have committed. The children [of Jerusalem] have been captured and taken [to other countries].
6 Diyar Sihiyona ba ta da sauran daraja.’Ya’yan sarakunanta sun zama kamar bareyi waɗanda suka rasa wurin kiwo; cikin rashin ƙarfi suka guje wa masu fafararsu.
Jerusalem was a beautiful city, but it is not beautiful now. The leaders [of the city] are like [SIM] deer that are starving because of being unable to find any grass [to eat]. They are very weak, with the result that they are unable to run from their enemies.
7 A cikin kwanakin da take shan wahala take kuma yawo Urushalima ta tuna da dukan dukiyar da take da ita a kwanakin dā can. Sa’ad da mutanenta suka faɗa cikin hannun abokan gābanta, ba wanda ya taimake ta. Maƙiyanta suka dube ta suka yi mata dariya don hallakar da ta auko mata.
[The people of] Jerusalem are sad and scattered, and they think about the previous greatness of the city. [But now] our enemies have captured the city, and there is no one to help the people. Our enemies destroyed the city and laughed while they were doing that.
8 Urushalima ta yi zunubi ƙwarai saboda haka ta zama marar tsarki. Dukan masu martaba ta sun raina ta, gama sun ga tsiraicinta; ita ma da kanta tana nishi da ƙyar ta kuma juya baya.
[The people of] [PRS] Jerusalem have sinned very much; [it is as though] [MET] the city has become [like] a filthy [rag]. All those who [previously] honored the city [now] despise it, because they see that it has become very disgraced [MET]. Now [the people of] the city groan, and they cover their faces [because they are very ashamed].
9 Ƙazantarta ta manne wa rigunanta; ba tă kula da nan gaba ba, fāɗuwarta kuwa babban abu ne; babu wanda zai yi mata ta’aziyya. “Duba, ya Ubangiji, ka ga wahalata, gama maƙiyi ya yi nasara.”
The city has become filthy because of [PRS] the sins that the people have committed; they did not think about what could happen to the city. [Now] the city has been destroyed, and there is no one to comfort [the people]. [The people cry out saying], “Yahweh, look at how we are suffering because our enemies have defeated us!”
10 Maƙiya ya kwashe dukiyarta duka; ta ga mutanen da ba su san Allah ba sun shiga wuri mai tsarkinta waɗanda ka hana su shiga taron jama’arka.
Our enemies have taken away all our treasures, all the valuable things that we owned. We have seen [soldiers from other] nations, [men who do not worship Yahweh], enter our sacred temple, [the place] where foreigners/non-Israelis were (forbidden/not allowed) to enter.
11 Dukan mutanenta suna nishi da ƙyar suna neman burodi; sun sayar da dukiyarsu don su samu abinci don kada su mutu da yunwa. “Ubangiji, ka duba ka gani, gama an yashe ni.”
The people of the city groan while they search for food; they have given their treasures to get food [to eat] to remain alive. [They say], “Yahweh, look [at us], and see that we are despised!”
12 “Ko wannan ba wani abu ba ne a wurinku, dukanku masu wucewa? Ku duba ku gani. Ko akwai wata wahala kamar irin wadda nake sha, wadda Ubangiji ya auko mini a cikin zafin fushinsa?
You people who pass by, you do not [RHQ] seem to care at all [about what has happened to us]. Look around and see that there are no other [RHQ] people who are suffering like we are. Yahweh has caused us to suffer because he was extremely angry [with us].
13 “Daga sama ya aiko da wuta, ya aiko ta cikin ƙasusuwana. Ya shimfiɗa raga a ƙafafuna ya juyo da ni. Ya bar ni ni kaɗai, sumamme dukan yini.
[It is as though] he sent a fire from heaven [MTY] that burned in our bones; [it is as though] [MET] he has placed a trap for our feet, and has prevented us from walking any further. He has abandoned us; we are weak/miserable [every day], all day long.
14 “Ya ɗaura zunubaina a wuyana; aka naɗe su a hannuwansa. Aka rataye su a wuyana Ubangiji ya kwashe ƙarfina. Ya bashe ni ga waɗanda suka fi ni ƙarfi.
He caused the sins that we have committed to be [like] a heavy load for us to carry; [it is as though] [MET] he tied them around our necks. Previously we were strong, but he has caused us to become weak. He has allowed our enemies to capture us, and we were not able to do anything to resist them.
15 “Ubangiji ya ƙi duk mayaƙan da suke tare da ni; ya sa wata runduna ta tayar mini ta kuma tattake samarina. Ubangiji ya tattake budurwa Diyar Yahuda kamar’ya’yan inabi a wurin matsewa.
Yahweh looked at our mighty soldiers and laughed at them. He has summoned a great army to [come and] crush our young soldiers. [It is as though] [MET] Yahweh has trampled on [us] people of Judah like [SIM] [people trample] on grapes in a pit [to make wine].
16 “Dalilin da ya sa nake kuka ke nan idanuna kuma suna ta zubar da hawaye. Babu wani a kusa da zai yi mini ta’aziyya, ba wanda zai sabunta ruhuna.’Ya’yana sun zama fakirai domin maƙiyina ya yi nasara.”
I weep because of [all] those things; my eyes are filled with tears. There is no one to comfort me; those who could encourage me are far away. Our enemies have conquered [us], so our children have nothing good to (hope for/expect to happen).
17 Sihiyona ta miƙa hannunta, amma ba wani da zai yi mata ta’aziyya. Ubangiji ya umarta cewa maƙwabtansa za su zama maƙiyansa; Urushalima ta zama abar ƙyama a cikinsu.
[We people of] [PRS] Jerusalem reach out our hands [to get help], but there is no one to comfort us. Yahweh has decided concerning [us descendants of] Jacob that the people in nearby nations will become our enemies; so they consider that Jerusalem has become [like] [MET] a filthy rag.
18 “Ubangiji mai adalci ne, duk da haka na yi tawaye da umarninsa. Ku saurara, jama’a duka; ku dubi wahalar da nake sha. Samarina da’yan matana duka sun tafi bauta.
But what Yahweh has done [to us] is fair, because we have rebelled against obeying the commands that he gave [us]. You people everywhere, listen [to us]; [look and] see that we are suffering [greatly]. We had [many] sons and daughters, but they have been captured and forced to go to distant countries.
19 “Na kira abokaina amma sun yashe ni. Firistocina da dattawana sun hallaka a cikin birnin yayinda suke neman abinci don kada su mutu da yunwa.
We pleaded with our allies [to help us], but they [all] refused. Our priests and our leaders have died [from hunger] in the city while they were searching for food [to eat] to remain alive.
20 “Duba, Ubangiji, ka ga ƙuncin da nake ciki! Ina shan azaba a raina, ba ni da kwanciyar rai a cikin zuciyata, domin na yi tawaye sosai. A waje takobi na kisa; a ciki kuma akwai mutuwa.
Yahweh, see that we are suffering very much. [It is as though] our inner beings are tormented. We are sad [SYN] because we have rebelled [against you]. Our enemies kill people in the streets with their swords; people are dying [because they have no food to eat].
21 “Mutane suna ji ina nishi da ƙyar, amma ba wanda zai yi mini ta’aziyya. Dukan maƙiyana sun ji wahalar da nake ciki; suna farin ciki da abin da ka yi. Ka kawo ranan nan da ka sanar domin su ma su zama kamar ni.
People have heard us while we groaned, but no one [came to] comfort us. [Yahweh, ] you caused us to experience this [disaster], and our enemies are happy to see what you have done [to us]. But cause it soon to be the time that you have promised, when our enemies will suffer like we have suffered!
22 “Bari ka ga muguntarsu duka; ka yi musu yadda ka yi mini domin dukan zunubansu. Nishina da yawa kuma zuciyata ta gaji.”
[Yahweh, ] see all the evil things that they have done and punish them! [Punish them] like you have punished us for all the sins that we committed! [We say this to you] because we suffer and groan very much, and we (faint/are very sad).

< Makoki 1 >