< Mahukunta 7 >

1 Kashegari da sassafe, Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) da dukan mutanensa suka kafa sansani a maɓulɓulan Harod. Sansanin Midiyawa kuma yana arewa da su a kwari kusa da tudu na More.
Potem je Jerubáal, ki je Gideón in vse ljudstvo, ki je bilo z njim, vstalo zgodaj in se utaborilo poleg vodnjaka Haród, tako da je bila vojska Midjáncev na njihovi severni strani, v dolini pri Moréjevem hribu.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Mutanen da kake da su sun yi mini yawa da zan ba da Midiyawa a hannunsu. Don kada Isra’ila tă yi mini fahariya cewa ƙarfinta ne ya cece su,
Gospod je rekel Gideónu: »Ljudstva, ki je s teboj, je zame preveč, da bi Midjánce izročil v njihove roke, da se ne bi Izrael poveličeval zoper mene, rekoč: ›Moja lastna roka me je rešila.‹«
3 ka yi shela ga mutane yanzu cewa, ‘Duk wanda ya yi rawan jiki don tsoro, sai yă juya yă bar Dutsen Gileyad.’” Saboda haka mutum dubu ashirin da biyu suka koma, sai mutum dubu goma suka rage.
Zdaj torej pojdi, razglasi v ušesa ljudstva, rekoč: ›Kdorkoli je boječ in se boji, naj se vrne in zgodaj odide z gore Gileád.‹« In tam se jih je izmed ljudstva vrnilo dvaindvajset tisoč, ostalo pa jih je deset tisoč.
4 Amma Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Har yanzu mutanen sun yi yawa. Ka kai cikin ruwa, in kuma tankaɗe maka su a can. In na ce, ‘Wannan zai tafi da kai,’ to, zai tafi; amma in na ce, ‘Wannan ba zai tafi da kai ba,’ to, ba zai tafi ba.”
Gospod je rekel Gideónu: »Ljudstva je še preveč. Privedi jih dol k vodi in tam ti jih bom preizkusil.« Zgodilo se bo, da o komer ti rečem: ›Ta bo šel s teboj, ‹ bo ta isti šel s teboj; in o komer ti rečem: ›Ta ne bo šel s teboj, ‹ ta isti ne bo šel.«
5 Saboda haka Gideyon ya kai mutanen cikin ruwa. A can Ubangiji ya ce masa, “Ka ware waɗanda suka tanɗi ruwa kamar kare daga waɗanda suka durƙusa suka sha ruwan.”
Tako je ljudstvo privedel dol k vodi in Gospod je rekel Gideónu: »Kdorkoli s svojim jezikom sreba vodo, kakor sreba pes, tega boš postavil poleg sebe, podobno vsakega, ki poklekne dol na svoja kolena, da bi pil.«
6 Mutum ɗari uku sun tanɗi ruwa, dukan sauran kuwa suka durƙusa suka sha ruwan.
Število tistih, ki so srebali s pristavljanjem svoje roke k svojim ustom, je bilo tristo mož, toda vsi drugi izmed ljudstva so se upognili na svoja kolena, da pijejo vodo.
7 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Da mutum ɗari uku ɗin nan da suka tanɗi ruwa, zan cece ka in kuma ba da Midiyawa a hannuwanku. Ka bar sauran mutane su tafi kowa zuwa wurinsa.”
Gospod je rekel Gideónu: »S tristo možmi, ki so srebali, vas bom rešil in Midjánce izročil v tvojo roko. Vse preostalo ljudstvo pa naj gre vsak mož k svojemu kraju.«
8 Saboda haka Gideyon ya mai da sauran Isra’ilawa zuwa tentinsu amma ya riƙe mutum ɗari uku waɗanda suka karɓi guzuri da ƙahonin sauran. To, sansanin Midiyawa yana ƙasa da su a kwarin.
Tako je ljudstvo v svojo roko vzelo živež in svoje šofarje, ves preostanek Izraela pa je vsakega moža poslal k svojemu šotoru in obdržal tistih tristo mož. Midjánska vojska pa je bila pod njim v dolini.
9 A daren nan Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Tashi ka tafi sansaninsu domin zan ba da su a hannuwanka.
Iste noči se je pripetilo, da mu je Gospod rekel: »Vstani, spusti se k vojski, kajti izročil sem jo v tvojo roko.
10 In kana tsoron fāɗa musu, sai ka tafi da bawanka Fura
Toda če se bojiš iti dol, pojdi dol k vojski s svojim služabnikom Purájem.
11 ka kuma saurari abin da suke faɗi. Bayan haka za ka sami ƙarfin hali ka auka musu.” Saboda haka sai ya tafi tare da Fura bawansa zuwa sansanin.
Slišal boš kaj govorijo. Potem se bodo tvoje roke okrepile, da greš dol k vojski.« Potem je s svojim služabnikom Purájem odšel dol k zunanjim izmed oboroženih mož, ki so bili v vojski.
12 Midiyawa, Amalekawa da dukan sauran mutane gabashi suka yi sansani a kwari, kamar fāra. Raƙumansu kuma kamar yashi a bakin teku don sun wuce ƙirge.
Midjánci in Amalečani in vsi otroci vzhoda pa so ležali povprek po dolini, zaradi množice podobni kobilicam in njihovih kamel je bilo zaradi množice brez števila, kakor peska ob morski obali.
13 Gideyon ya iso daidai wani yana faɗa wa wani aboki mafarkinsa, yana cewa, “Na yi mafarki, na ga dunƙule burodin sha’ir ya fāɗo a tsakiyar sansanin Midiyawa. Ya bugi tentin da ƙarfin da ya sa tenti ta kife a ƙasa.”
Ko je Gideón prišel, glej, je bil tam mož, ki je svojemu tovarišu povedal sanje ter rekel: »Glej, sanjal sem sanje in glej, kolač ječmenovega kruha se je privalil v midjánsko vojsko, prišel k šotoru in ga udaril, da je ta padel in ga prevrnil, da je ležal postrani.«
14 Abokinsa ya ce, “Ai wannan ba wani abu ba ne fiye da takobin Gideyon ɗan Yowash, mutumin Isra’ila. Allah ya ba da Midiyawa da dukan sansani a hannuwansa.”
Njegov tovariš je odgovoril in rekel: »To ni nič drugega kakor meč Gideóna, Joáševega sina, moža iz Izraela, kajti v njegovo roko je Bog izročil Midjánce in vso vojsko.«
15 Da Gideyon ya ji mafarkin da fassararsa, sai ya yi wa Allah sujada. Ya koma sansanin Isra’ila ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku tashi! Ubangiji ya ba da sansanin Midiyawa a hannuwanku.”
Bilo je tako, ko je Gideón slišal pripovedovanje sanj in njeno razlago, da je oboževal, se vrnil v Izraelovo vojsko in rekel: »Vstanite, kajti Gospod je v vašo roko izročil midjánsko vojsko.«
16 Ya raba mutum ɗari uku ɗin kashi uku, ya ba kowannensu ƙaho da tulu da acibalbal a ciki.
Tristo mož je razdelil na tri skupine in v roko vsakega moža položil šofar s praznimi lončenimi vrči in svetilkami znotraj vrčev.
17 Ya ce musu, “Ku dube ni, ku bi abin da na yi. Sa’ad da na kai sansanin, ku yi daidai abin da na yi.
Rekel jim je: »Glejte mene in storite podobno. In glejte, ko pridem k robu tabora, se bo zgodilo, da kakor storim jaz, boste tako storili tudi vi.
18 Sa’ad da ni da dukan waɗanda suke tare da ni muka busa ƙahoninmu, to, ko’ina a kewayen sansanin sai ku busa naku ku kuma yi ihu, ku ce, ‘Don Ubangiji da kuma domin Gideyon.’”
Ko zatrobim s šofarjem, jaz in vsi tisti, ki so z menoj, potem tudi vi zatrobite s šofarji na vsaki strani tabora in recite: › Meč od Gospoda in od Gideóna.‹«
19 Gideyon da mutum ɗari da suke tare da shi suka kai sansanin da tsakar dare bayan an sauya matsara. Suka busa ƙahoninsu, suka farfashe tulunansu da suke hannuwansu.
Tako so Gideón in sto mož, ki so bili z njim, prišli k robu tabora na začetku srednje straže in imeli so ravno sveže postavljeno stražo. Zatrobili so na šofarje in razbili lončene vrče, ki so bili v njihovih rokah.
20 Ƙungiyoyi uku ɗin nan suka busa ƙahonin, suka fasa tuluna. Suka ɗauki acibalbal a hannuwansu na hagu da ƙahonin busawa a hannuwansu na dama, sai suka yi ihu, “Takobi don Ubangiji da kuma don Gideyon!”
Tri skupine so trobile na šofarje in razbile lončene vrče in držale svetilke v svojih levicah in šofarje v svojih desnicah, da z njimi trobijo in kričali: »Meč od Gospoda in od Gideóna.«
21 Yayinda kowannensu ya tsaya a inda yake kewaye da sansanin, dukan Midiyawa suka fito da gudu, suna kuka yayinda suke gudu.
Stali so vsak mož na svojem mestu okoli tabora in vsa vojska je stekla, kričala in pobegnila.
22 Sa’ad da aka busa ƙahonin nan ɗari uku sai Ubangiji ya sa Midiyawa suka yi ta saran juna. Mayaƙan suka gudu zuwa Bet-Shitta wajen Zerera har zuwa yankin Abel-Mehola kusa da Tabbat.
Tristo [jih] je trobilo na šofarje in Gospod je torej po vsej vojski naravnal meč vsakega moža zoper svojega tovariša in vojska je pobegnila do Bet Šite v Cerédi in do meje Abél Mehóle, do Tabáta.
23 Aka kira dukan Isra’ilawa daga Naftali, Asher da dukan Manasse, suka kuwa fatattaki Midiyawa.
Izraelovi možje so se zbrali skupaj iz Neftálija, iz Aserja, iz vsega Manáseja in zasledovali Midjánce.
24 Gideyon ya aiki manzanni zuwa dukan ƙasar tudu ta Efraim cewa, “Ku gangaro ku yaƙi Midiyawa ku ƙwace ruwan Urdun gaba da su har zuwa Bet-Bara.” Saboda haka aka kira dukan mutanen Efraim suka ƙwace ruwan Urdun har zuwa Bet-Bara.
Gideón je poslal poslance po vsej gori Efrájim, rekoč: »Pridite dol zoper Midjánce in pred njimi zasedite vode do Bet Bare in Jordana.« Potem so se vsi Efrájimovi možje zbrali skupaj in zasedli vode do Bet Bare in Jordana.
25 Suka kuma kama shugabannin biyu na Midiyawa, Oreb da Zeyib suka kashe Oreb a dutsen Oreb, Zeyib kuma a wurin matsin ruwa inabin Zeyib. Suka fatattaki Midiyawa suka kawo kawunan Oreb da Zeba wurin Gideyon, wanda yake kusa da Urdun.
Zajeli so dva princa izmed Midjáncev, Oréba in Zeéba. Oréba so usmrtili na Orébovi skali, Zeéba pa so usmrtili na Zeébovi vinski stiskalnici in zasledovali Midjánce ter glavi Oréba in Zeéba prinesli Gideónu, na drugo stran Jordana.

< Mahukunta 7 >