< Mahukunta 7 >

1 Kashegari da sassafe, Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) da dukan mutanensa suka kafa sansani a maɓulɓulan Harod. Sansanin Midiyawa kuma yana arewa da su a kwari kusa da tudu na More.
Jérobaal, qui est Gédéon, avec tout le peuple qui était avec lui, se leva de bon matin et alla camper au-dessus de la source de Harad. Le camp de Madian était au nord de celui de Gédéon, vers la colline de Moré, dans la plaine.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Mutanen da kake da su sun yi mini yawa da zan ba da Midiyawa a hannunsu. Don kada Isra’ila tă yi mini fahariya cewa ƙarfinta ne ya cece su,
Yahweh dit à Gédéon: « Le peuple que tu as avec toi est trop nombreux pour que je livre Madian entre ses mains, de peur qu’Israël n’en tire gloire contre moi, en disant: C’est ma main qui m’a délivré.
3 ka yi shela ga mutane yanzu cewa, ‘Duk wanda ya yi rawan jiki don tsoro, sai yă juya yă bar Dutsen Gileyad.’” Saboda haka mutum dubu ashirin da biyu suka koma, sai mutum dubu goma suka rage.
Fais donc publier ceci aux oreilles du peuple: Que celui qui a peur et qui tremble s’en retourne et se retire de la montagne de Gelboé. » Vingt-deux mille hommes parmi le peuple s’en retournèrent, et il en resta dix mille.
4 Amma Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Har yanzu mutanen sun yi yawa. Ka kai cikin ruwa, in kuma tankaɗe maka su a can. In na ce, ‘Wannan zai tafi da kai,’ to, zai tafi; amma in na ce, ‘Wannan ba zai tafi da kai ba,’ to, ba zai tafi ba.”
Yahweh dit à Gédéon: « Le peuple est encore trop nombreux. Fais-les descendre près de l’eau, et là je t’en ferai un triage. Celui dont je te dirai: Qu’il aille avec toi, ira avec toi; et celui dont je te dirai: Qu’il n’aille pas avec toi, n’ira pas avec toi. »
5 Saboda haka Gideyon ya kai mutanen cikin ruwa. A can Ubangiji ya ce masa, “Ka ware waɗanda suka tanɗi ruwa kamar kare daga waɗanda suka durƙusa suka sha ruwan.”
Gédéon fit descendre le peuple près de l’eau, et Yahweh dit à Gédéon: « Tous ceux qui laperont l’eau avec la langue, comme lape le chien, mets-les à part; de même tous ceux qui se mettront à genoux pour boire. »
6 Mutum ɗari uku sun tanɗi ruwa, dukan sauran kuwa suka durƙusa suka sha ruwan.
Ceux qui lapèrent l’eau dans leur main, en la portant à leur bouche, furent au nombre de trois cents hommes; tout le reste du peuple s’était mis à genoux pour boire.
7 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Da mutum ɗari uku ɗin nan da suka tanɗi ruwa, zan cece ka in kuma ba da Midiyawa a hannuwanku. Ka bar sauran mutane su tafi kowa zuwa wurinsa.”
Et Yahweh dit à Gédéon: « C’est avec ces trois cents hommes qui ont lapé que je vous sauverai et que je livrerai Madian entre tes mains; que tout le reste du peuple s’en aille chacun chez soi. »
8 Saboda haka Gideyon ya mai da sauran Isra’ilawa zuwa tentinsu amma ya riƙe mutum ɗari uku waɗanda suka karɓi guzuri da ƙahonin sauran. To, sansanin Midiyawa yana ƙasa da su a kwarin.
Les trois cents prirent des vivres du peuple et ses trompettes; puis Gédéon renvoya tout le reste des hommes d’Israël chacun dans sa tente, et il garda les trois cents hommes. Le camp des Madianites était au-dessous de lui, dans la plaine.
9 A daren nan Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Tashi ka tafi sansaninsu domin zan ba da su a hannuwanka.
Pendant cette nuit, Yahweh dit à Gédéon: « Lève-toi, descends au camp, car je l’ai livré entre tes mains.
10 In kana tsoron fāɗa musu, sai ka tafi da bawanka Fura
Si tu crains de l’attaquer, descends avec Phara, ton serviteur;
11 ka kuma saurari abin da suke faɗi. Bayan haka za ka sami ƙarfin hali ka auka musu.” Saboda haka sai ya tafi tare da Fura bawansa zuwa sansanin.
tu écouteras ce qu’ils disent, et ensuite tes mains seront fortifiées et tu descendras sans crainte au camp. » Il descendit avec Phara, son serviteur, jusqu’aux avant-postes du camp.
12 Midiyawa, Amalekawa da dukan sauran mutane gabashi suka yi sansani a kwari, kamar fāra. Raƙumansu kuma kamar yashi a bakin teku don sun wuce ƙirge.
— Madian, Amalec et tous les fils de l’Orient étaient répandus dans la plaine, nombreux comme les sauterelles, et leurs chameaux étaient sans nombre comme le sable sur le bord de la mer. —
13 Gideyon ya iso daidai wani yana faɗa wa wani aboki mafarkinsa, yana cewa, “Na yi mafarki, na ga dunƙule burodin sha’ir ya fāɗo a tsakiyar sansanin Midiyawa. Ya bugi tentin da ƙarfin da ya sa tenti ta kife a ƙasa.”
Gédéon arriva, et voici qu’un homme racontait à son camarade un songe; il disait: « J’ai eu un songe et voici: un pain d’orge roulait dans le camp de Madian; il vint jusqu’à la tente, la heurta, et elle tomba; il l’a renversée sens dessus dessous, et la tente est tombée. »
14 Abokinsa ya ce, “Ai wannan ba wani abu ba ne fiye da takobin Gideyon ɗan Yowash, mutumin Isra’ila. Allah ya ba da Midiyawa da dukan sansani a hannuwansa.”
Son camarade répondit et dit: « Ce n’est pas autre chose que l’épée de Gédéon, fils de Joas, homme d’Israël; Dieu a livré entre ses mains Madian et tout le camp. »
15 Da Gideyon ya ji mafarkin da fassararsa, sai ya yi wa Allah sujada. Ya koma sansanin Isra’ila ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku tashi! Ubangiji ya ba da sansanin Midiyawa a hannuwanku.”
Lorsque Gédéon eut entendu le récit du songe et son explication, il se prosterna et, étant revenu au camp d’Israël, il dit: « Levez-vous, car Yahweh a livré entre nos mains le camp de Madian. »
16 Ya raba mutum ɗari uku ɗin kashi uku, ya ba kowannensu ƙaho da tulu da acibalbal a ciki.
Il divisa en trois colonnes les trois cents hommes, et leur remit à tous des trompettes et des cruches vides, avec des flambeaux dans les cruches,
17 Ya ce musu, “Ku dube ni, ku bi abin da na yi. Sa’ad da na kai sansanin, ku yi daidai abin da na yi.
et il leur dit: « Vous me regarderez, et vous ferez comme moi. Dès que j’arriverai aux abords du camp, vous ferez ce que je ferai.
18 Sa’ad da ni da dukan waɗanda suke tare da ni muka busa ƙahoninmu, to, ko’ina a kewayen sansanin sai ku busa naku ku kuma yi ihu, ku ce, ‘Don Ubangiji da kuma domin Gideyon.’”
Quand je sonnerai de la trompette, moi et tous ceux qui sont avec moi, vous aussi vous sonnerez de la trompette tout autour du camp, et vous direz: Pour Yahweh et pour Gédéon! »
19 Gideyon da mutum ɗari da suke tare da shi suka kai sansanin da tsakar dare bayan an sauya matsara. Suka busa ƙahoninsu, suka farfashe tulunansu da suke hannuwansu.
Gédéon et les cent hommes qui étaient avec lui arrivèrent aux abords du camp au commencement de la veille du milieu, comme on venait de relever les sentinelles; ils sonnèrent de la trompette et brisèrent les cruches qu’ils avaient à la main.
20 Ƙungiyoyi uku ɗin nan suka busa ƙahonin, suka fasa tuluna. Suka ɗauki acibalbal a hannuwansu na hagu da ƙahonin busawa a hannuwansu na dama, sai suka yi ihu, “Takobi don Ubangiji da kuma don Gideyon!”
Alors les trois corps sonnèrent de la trompette et brisèrent les cruches et, saisissant les flambeaux de la main gauche, et de la droite les trompettes pour en sonner, ils s’écrièrent: « Epée pour Yahweh et pour Gédéon! »
21 Yayinda kowannensu ya tsaya a inda yake kewaye da sansanin, dukan Midiyawa suka fito da gudu, suna kuka yayinda suke gudu.
Ils restèrent chacun à sa place autour du camp; et tout le camp se mit à courir, à crier et à fuir.
22 Sa’ad da aka busa ƙahonin nan ɗari uku sai Ubangiji ya sa Midiyawa suka yi ta saran juna. Mayaƙan suka gudu zuwa Bet-Shitta wajen Zerera har zuwa yankin Abel-Mehola kusa da Tabbat.
Pendant que les trois cents hommes sonnaient de la trompette, Yahweh fit tourner aux Madianites l’épée les uns contre les autres et contre tout le camp. Le camp s’enfuit jusqu’à Beth-Setta vers Saréra, jusqu’au bord d’Abel-Méhula, près de Tebbath.
23 Aka kira dukan Isra’ilawa daga Naftali, Asher da dukan Manasse, suka kuwa fatattaki Midiyawa.
Les hommes d’Israël se rassemblèrent, ceux de Nephthali, d’Aser et de tout Manassé, et ils poursuivirent Madian.
24 Gideyon ya aiki manzanni zuwa dukan ƙasar tudu ta Efraim cewa, “Ku gangaro ku yaƙi Midiyawa ku ƙwace ruwan Urdun gaba da su har zuwa Bet-Bara.” Saboda haka aka kira dukan mutanen Efraim suka ƙwace ruwan Urdun har zuwa Bet-Bara.
Gédéon envoya des messagers dans toute la montagne d’Ephraïm, pour dire: « Descendez à la rencontre de Madian, et occupez avant eux le passage des eaux jusqu’à Bethbéra, ainsi que les gués du Jourdain. » Tous les hommes d’Ephraïm se rassemblèrent, et ils occupèrent les eaux jusqu’à Bethbéra, ainsi que les gués du Jourdain.
25 Suka kuma kama shugabannin biyu na Midiyawa, Oreb da Zeyib suka kashe Oreb a dutsen Oreb, Zeyib kuma a wurin matsin ruwa inabin Zeyib. Suka fatattaki Midiyawa suka kawo kawunan Oreb da Zeba wurin Gideyon, wanda yake kusa da Urdun.
Ayant saisi deux princes de Madian, Oreb et Zeb, ils tuèrent Oreb au rocher d’Oreb, et ils tuèrent Zeb au pressoir de Zeb. Ils poursuivirent Madian, et ils apportèrent les têtes d’Oreb et de Zeb à Gédéon, de l’autre côté du Jourdain.

< Mahukunta 7 >