< Mahukunta 7 >

1 Kashegari da sassafe, Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) da dukan mutanensa suka kafa sansani a maɓulɓulan Harod. Sansanin Midiyawa kuma yana arewa da su a kwari kusa da tudu na More.
And Jerubba‘al (he [is] Gideon) rises early, and all the people who [are] with him, and they encamp by the well of Harod, and the camp of Midian has been on the south of him, on the height of Moreh, in the valley.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Mutanen da kake da su sun yi mini yawa da zan ba da Midiyawa a hannunsu. Don kada Isra’ila tă yi mini fahariya cewa ƙarfinta ne ya cece su,
And YHWH says to Gideon, “The people who [are] with you [are] too many for My giving Midian into their hand, lest Israel beautify itself against Me, saying, My hand has given salvation to me;
3 ka yi shela ga mutane yanzu cewa, ‘Duk wanda ya yi rawan jiki don tsoro, sai yă juya yă bar Dutsen Gileyad.’” Saboda haka mutum dubu ashirin da biyu suka koma, sai mutum dubu goma suka rage.
and now, please call in the ears of the people, saying, Whoever [is] afraid and trembling, let him turn back and go early from Mount Gilead”; and there return twenty-two thousand of the people, and ten thousand have been left.
4 Amma Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Har yanzu mutanen sun yi yawa. Ka kai cikin ruwa, in kuma tankaɗe maka su a can. In na ce, ‘Wannan zai tafi da kai,’ to, zai tafi; amma in na ce, ‘Wannan ba zai tafi da kai ba,’ to, ba zai tafi ba.”
And YHWH says to Gideon, “The people [are] yet too many; bring them down to the water, and I refine him for you there; and it has been, he of whom I say to you, This goes with you—he goes with you; and any of whom I say to you, This does not go with you—he does not go.”
5 Saboda haka Gideyon ya kai mutanen cikin ruwa. A can Ubangiji ya ce masa, “Ka ware waɗanda suka tanɗi ruwa kamar kare daga waɗanda suka durƙusa suka sha ruwan.”
And he brings the people down to the water, and YHWH says to Gideon, “Everyone who laps of the water with his tongue as the dog laps—you set him apart; also everyone who bows on his knees to drink.”
6 Mutum ɗari uku sun tanɗi ruwa, dukan sauran kuwa suka durƙusa suka sha ruwan.
And the number of those lapping with their hand to their mouth is three hundred men, and all the rest of the people have bowed down on their knees to drink water.
7 Sai Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Da mutum ɗari uku ɗin nan da suka tanɗi ruwa, zan cece ka in kuma ba da Midiyawa a hannuwanku. Ka bar sauran mutane su tafi kowa zuwa wurinsa.”
And YHWH says to Gideon, “I save you by the three hundred men who are lapping, and have given Midian into your hand, and all the people go, each to his place.”
8 Saboda haka Gideyon ya mai da sauran Isra’ilawa zuwa tentinsu amma ya riƙe mutum ɗari uku waɗanda suka karɓi guzuri da ƙahonin sauran. To, sansanin Midiyawa yana ƙasa da su a kwarin.
And the people take the provision in their hand, and their horns, and he has sent every man of Israel away, each to his tents; and he has kept hold on the three hundred men, and the camp of Midian has been by him at the lower part of the valley.
9 A daren nan Ubangiji ya ce wa Gideyon, “Tashi ka tafi sansaninsu domin zan ba da su a hannuwanka.
And it comes to pass, on that night, that YHWH says to him, “Rise, go down into the camp, for I have given it into your hand;
10 In kana tsoron fāɗa musu, sai ka tafi da bawanka Fura
and if you are afraid to go down—go down, you and your young man Phurah, to the camp,
11 ka kuma saurari abin da suke faɗi. Bayan haka za ka sami ƙarfin hali ka auka musu.” Saboda haka sai ya tafi tare da Fura bawansa zuwa sansanin.
and you have heard what they speak, and afterward your hands are strengthened, and you have gone down against the camp.” And he goes down, he and his young man Phurah, to the extremity of the fifties who [are] in the camp;
12 Midiyawa, Amalekawa da dukan sauran mutane gabashi suka yi sansani a kwari, kamar fāra. Raƙumansu kuma kamar yashi a bakin teku don sun wuce ƙirge.
and Midian, and Amalek, and all the sons of the east are lying in the valley, as the locust for multitude, and of their camels there is no number, as sand which [is] on the seashore for multitude.
13 Gideyon ya iso daidai wani yana faɗa wa wani aboki mafarkinsa, yana cewa, “Na yi mafarki, na ga dunƙule burodin sha’ir ya fāɗo a tsakiyar sansanin Midiyawa. Ya bugi tentin da ƙarfin da ya sa tenti ta kife a ƙasa.”
And Gideon comes in, and behold, a man is recounting a dream to his companion, and says, “Behold, I have dreamed a dream, and behold, a cake of barley-bread is turning itself over into the camp of Midian, and it comes to the tent, and strikes it, and it falls, and turns it upwards, and the tent has fallen.”
14 Abokinsa ya ce, “Ai wannan ba wani abu ba ne fiye da takobin Gideyon ɗan Yowash, mutumin Isra’ila. Allah ya ba da Midiyawa da dukan sansani a hannuwansa.”
And his companion answers and says, “This is nothing except the sword of Gideon son of Joash, a man of Israel; God has given Midian and all the camp into his hand.”
15 Da Gideyon ya ji mafarkin da fassararsa, sai ya yi wa Allah sujada. Ya koma sansanin Isra’ila ya yi kira da ƙarfi ya ce, “Ku tashi! Ubangiji ya ba da sansanin Midiyawa a hannuwanku.”
And it comes to pass, when Gideon hears the narration of the dream and its interpretation, that he bows himself, and turns back to the camp of Israel, and says, “Rise, for YHWH has given the camp of Midian into your hand.”
16 Ya raba mutum ɗari uku ɗin kashi uku, ya ba kowannensu ƙaho da tulu da acibalbal a ciki.
And he divides the three hundred men [into] three detachments, and puts horns into the hand of all of them, and empty pitchers, and lamps within the pitchers.
17 Ya ce musu, “Ku dube ni, ku bi abin da na yi. Sa’ad da na kai sansanin, ku yi daidai abin da na yi.
And he says to them, “Look at me, and thus do; and behold, I am coming into the extremity of the camp—and it has been—as I do so you do;
18 Sa’ad da ni da dukan waɗanda suke tare da ni muka busa ƙahoninmu, to, ko’ina a kewayen sansanin sai ku busa naku ku kuma yi ihu, ku ce, ‘Don Ubangiji da kuma domin Gideyon.’”
and I have blown with a horn—I and all who [are] with me, and you have blown with horns, even you, around all the camp, and have said, For YHWH and for Gideon!”
19 Gideyon da mutum ɗari da suke tare da shi suka kai sansanin da tsakar dare bayan an sauya matsara. Suka busa ƙahoninsu, suka farfashe tulunansu da suke hannuwansu.
And Gideon comes—and the hundred men who [are] with him—into the extremity of the camp, [at] the beginning of the middle watch (they had just posted watchmen), and they blow with horns—also dashing in pieces the pitchers which [are] in their hand;
20 Ƙungiyoyi uku ɗin nan suka busa ƙahonin, suka fasa tuluna. Suka ɗauki acibalbal a hannuwansu na hagu da ƙahonin busawa a hannuwansu na dama, sai suka yi ihu, “Takobi don Ubangiji da kuma don Gideyon!”
and the three detachments blow with horns, and break the pitchers, and keep hold with their left hand on the lamps, and with their right hand on the horns to blow, and they cry, “The sword of YHWH and of Gideon!”
21 Yayinda kowannensu ya tsaya a inda yake kewaye da sansanin, dukan Midiyawa suka fito da gudu, suna kuka yayinda suke gudu.
And they each stand in his place, around the camp, and all the camp runs, and they shout, and flee;
22 Sa’ad da aka busa ƙahonin nan ɗari uku sai Ubangiji ya sa Midiyawa suka yi ta saran juna. Mayaƙan suka gudu zuwa Bet-Shitta wajen Zerera har zuwa yankin Abel-Mehola kusa da Tabbat.
and the three hundred blow the horns, and YHWH sets the sword of each against his companion, even through all the camp; and the camp flees to Beth-Shittah, at Zererath, to the border of Abel-Meholah, by Tabbath.
23 Aka kira dukan Isra’ilawa daga Naftali, Asher da dukan Manasse, suka kuwa fatattaki Midiyawa.
And the men of Israel are called from Naphtali, and from Asher, and from all Manasseh, and pursue after Midian.
24 Gideyon ya aiki manzanni zuwa dukan ƙasar tudu ta Efraim cewa, “Ku gangaro ku yaƙi Midiyawa ku ƙwace ruwan Urdun gaba da su har zuwa Bet-Bara.” Saboda haka aka kira dukan mutanen Efraim suka ƙwace ruwan Urdun har zuwa Bet-Bara.
And Gideon has sent messengers into all the hill-country of Ephraim, saying, “Come down to meet Midian, and capture the waters from them as far as Beth-Barah, and the Jordan”; and every man of Ephraim is called, and they capture the waters as far as Beth-Barah, and the Jordan,
25 Suka kuma kama shugabannin biyu na Midiyawa, Oreb da Zeyib suka kashe Oreb a dutsen Oreb, Zeyib kuma a wurin matsin ruwa inabin Zeyib. Suka fatattaki Midiyawa suka kawo kawunan Oreb da Zeba wurin Gideyon, wanda yake kusa da Urdun.
and they capture two of the heads of Midian, Oreb and Zeeb, and slay Oreb at the rock of Oreb, and they have slain Zeeb at the wine-vat of Zeeb, and they pursue into Midian; and they have brought the heads of Oreb and Zeeb to Gideon beyond the Jordan.

< Mahukunta 7 >