< Mahukunta 6 >

1 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, sai ya ba da su ga Midiyawa shekara bakwai.
Les enfants d’Israël firent ce qui est mal aux yeux de Yahweh, et Yahweh les livra entre les mains de Madian, pendant sept ans.
2 Da Midiyawa suka matsa musu sosai, sai Isra’ilawa suka yi wa kansu mafakai a rammukan duwatsu, kogona da kuma mafaka.
La main de Madian fut puissante contre Israël. A cause de Madian, les enfants d’Israël se firent les antres qui sont dans les montagnes, les cavernes et les hauteurs fortifiées.
3 Duk lokacin da Isra’ilawa suka yi shuka sai Midiyawa da Amalekawa da waɗansu mutane daga gabashi sukan kai musu hari.
Quand Israël avait semé, Madian montait avec Amalec et les fils de l’Orient, et ils marchaient contre lui.
4 Sukan yi sansani a ƙasar sun lalatar da hatsi har zuwa Gaza kuma ba sa barin wani abu mai rai wa Isra’ila, ko tumaki ko shanu ko jakuna.
Campés en face d’Israël, ils dévastaient les productions de le terre jusque prés de Gaza, et ne laissaient aucune subsistance en Israël, ni brebis, ni bœufs, ni ânes.
5 Sukan zo da dabbobinsu da tentinsu kamar tarin fāri. Yana da wuya a ƙidaya yawan mutanen da kuma raƙumansu; sukan mamaye ƙasar don su lalatar da ita.
Car ils montaient avec leurs troupeaux et leurs tentes, et venaient nombreux comme des nuées de sauterelles; eux et leurs chameaux étaient innombrables, et ils venaient dans le pays pour le dévaster.
6 Midiyawa suka talauce Isra’ilawa ƙwarai, har ya sa suka yi kuka ga Ubangiji don taimako.
Israël fut très affaibli à cause de Madian, et les enfants d’Israël crièrent vers Yahweh.
7 Sa’ad da Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji saboda Midiyawa,
Lorsque les enfants d’Israël eurent crié vers Yahweh au sujet de Madian,
8 sai ya aika musu da annabi, wanda ya ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce na fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta.
Yahweh envoya un prophète aux enfants d’Israël. Il leur dit: « Ainsi parle Yahweh le Dieu d’Israël: Je vous ai fait monter de l’Égypte, et je vous ai fait sortir de la maison de servitude.
9 Na ƙwace ku daga ikon Masarawa da kuma daga dukan hannuwan masu danniya. Na kore su a gabanku na kuma ba ku ƙasarsu.
Je vous ai délivrés de la main des Egyptiens et de la main de tous vos oppresseurs; je les ai chassés devant vous, et je vous ai donné leur pays.
10 Na ce muku, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku; kada ku bauta allolin Amoriyawa, waɗanda kuke zama a ƙasarsu.’ Amma ba ku saurare ni ba.”
Je vous ai dit: je suis Yahweh, votre Dieu; vous ne craindrez pas les dieux des Amorrhéens dans le pays desquels vous habitez. Mais vous n’avez pas écouté ma voix. »
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya zo ya zauna a ƙarƙashin itacen oak a Ofra na Yowash mutumin Abiyezer, inda ɗansa Gideyon yake sussukar alkama a wurin matsin inabi don yă ɓoye daga Midiyawa.
Et l’Ange de Yahweh vint, et il s’assit sous le térébinthe d’Ephra, qui apporterait à Joas, de la famille d’Abiéser. Gédéon, son fils, battait le froment dans le pressoir, pour le mettre à l’abri de Madian.
12 Sa’ad da mala’ikan Ubangiji ya bayyana wa Gideyon, sai ya ce masa, “Ubangiji yana tare da kai, jarumi.”
L’Ange de Yahweh lui apparut et lui dit: « Yahweh est avec toi, vaillant héros. »
13 Gideyon ya ce, “Ranka yă daɗe, in Ubangiji yana tare da mu, me ya sa waɗannan abubuwa suka faru da mu? Ina dukan abubuwan al’ajabinsa waɗanda kakanninmu suka gaya mana game su sa’ad da suka ce, ‘Ashe, ba Ubangiji ne ya fitar da mu daga Masar ba?’ Amma yanzu Ubangiji ya rabu da mu ya kuma sa mu hannun Midiyawa.”
Gédéon lui dit: « Ah! mon seigneur, si Yahweh est avec nous, pourquoi toutes ces choses nous sont-elles arrivées? Et où sont tous ses prodiges que nos pères nous ont racontés, en disant: Yahweh ne nous a-t-il pas fait monter de l’Égypte? Et maintenant Yahweh nous abandonne et nous livre entre les mains de Madian. »
14 Sai Ubangiji ya juya wajensa ya ce, “Ka je da ƙarfin da kake da shi ka ceci Isra’ila daga hannun Midiyawa. Ba Ni ne nake aikan ka ba?”
Yahweh se tourna vers lui et dit: « Va avec cette force que tu as, et délivre Israël de la main de Madian; ne t’ai-je pas envoyé? »
15 Gideyon ya ce, “Amma Ubangiji, yaya zan iya ceci Isra’ila? Kabilata ce marar ƙarfi duka a Manasse, kuma ni ne ƙarami a iyalina.”
Gédéon lui dit: « Ah! Seigneur, avec quoi délivrerai-je Israël? Voici, ma famille est la plus pauvre en Manassé, et je suis le plus petit dans la maison de mon père. »
16 Ubangiji ya ce, “Zan kasance tare da kai, za ka kuwa fatattake dukan Midiyawa gaba ɗaya.”
Yahweh lui dit: « Je serai avec toi, et tu battras Madian comme un seul homme. »
17 Gideyon ya ce, “In lalle na sami tagomashi a gabanka, to, ka ba ni wata alamar da ta nuna lalle kai kake magana da ni.
Gédéon lui dit: « Si j’ai trouvé grâce à vos yeux, donnez-moi un signe que c’est vous qui me parlez.
18 Ina roƙonka ka dakata har in komo in kawo maka hadayata in ajiye a gabanka.” Sai Ubangiji ya ce, “Zan jira har ka dawo.”
Ne vous éloignez pas d’ici jusqu’à ce que je revienne auprès de vous, que j’apporte mon offrande et que je la dépose devant vous. » Et Yahweh dit: « Je resterai jusqu’à ce que tu reviennes. »
19 Sai Gideyon ya shiga ciki, ya gyara’yar akuya ya dafa, da garin efa ya yi burodi marar yisti. Da ya sa naman a kwando, romon kuma a tukunya, sai ya fito da su waje ya miƙa masa su a ƙarƙashin itacen oak.
Gédéon, étant entré, apprêta un chevreau et, avec un épha de farine, il fit des pains sans levain; puis, ayant mis la chair dans une corbeille et le jus dans un vase, il les lui apporta sous le térébinthe et les lui offrit.
20 Mala’ikan Allah ya ce masa, “Ka ɗauko naman da burodi marar yisti ka sa su a kan wannan dutse, ka zuba romon a kai.” Gideyon kuwa ya yi haka.
L’Ange de Yahweh lui dit: « Prends la chair et les pains sans levain, pose-les sur ce rocher, et verse le jus. » Et il fit ainsi.
21 Da kan sandan da yake a hannunsa, mala’ikan Ubangiji ya taɓa naman da burodi marar yistin. Sai wuta ta fito daga dutsen ta cinye naman da burodin. Mala’ikan kuwa ya ɓace.
L’Ange de Yahweh étendit l’extrémité du bâton qu’il avait à la main, et toucha la chair et les pains sans levain. Aussitôt le feu s’éleva du rocher, et consuma la chair et les pains sans levain, et l’Ange de Yahweh disparut à ses yeux.
22 Sa’ad da Gideyon ya gane mala’ikan Ubangiji ne, sai ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka! Na ga mala’ikan Ubangiji ido da ido.”
Gédéon vit que c’était l’Ange de Yahweh et Gédéon dit: « Malheur à moi, Seigneur Yahweh, car j’ai vu l’Ange de Yahweh face à face. »
23 Amma Ubangiji ya ce masa, “Salama! Kada ka ji tsoro, ba za ka mutu ba.”
Yahweh lui dit: « Sois en paix, ne crains point, tu ne mourras pas. »
24 Saboda haka Gideyon ya gina wa Ubangiji bagade a can, ya kuma kira shi, Ubangiji Salama ne. Har wa yau bagaden yana a Ofra ta mutanen Abiyezer.
Gédéon bâtit là un autel à Yahweh et l’appela: « Yahweh-Schalôm; » cet autel existe encore aujourd’hui à Ephra d’Abiéser.
25 A wannan dare Ubangiji ya ce masa, “Ka ɗauki bijimi na biyu daga garken mahaifinka, wannan mai shekara bakwai. Ka rushe bagaden mahaifinka na Ba’al ka sare ginshiƙin Ashera kusa da ita.
Cette nuit-là, Yahweh dit à Gédéon: « Prends le jeune taureau de ton père, et le second taureau de sept ans. Renverse l’autel de Baal qui est à ton père, et coupe l’aschéra qui est auprès.
26 Sa’an nan ka gina bagade irin da ya dace wa Ubangiji Allahnka a kan wannan tudu. Ka yi amfani da itacen katakon ginshiƙin Ashera da ka sare, ka miƙa bijiman nan biyu hadaya ta ƙonawa.”
Tu bâtiras ensuite, au sommet de ce lieu fort, un autel à Yahweh, ton Dieu, et tu le disposeras; tu prendras le second taureau et tu offriras un holocauste avec le bois de l’aschéra que tu auras coupée. »
27 Saboda haka Gideyon ya ɗebi bayinsa bakwai ya yi yadda Ubangiji ya ce masa. Amma saboda yana tsoron iyalinsa da mutanen gari, ya yi haka da dare a maimako da rana.
Gédéon prit dix hommes parmi ses serviteurs, et exécuta ce que Yahweh lui avait dit: mais, comme il n’osait le faire de jour par crainte de la maison de son père et des gens de la ville, il le fit de nuit.
28 Da safe sa’ad da mutanen garin suka tashi, sai suka tarar an rushe bagaden Ba’al, tare da ginshiƙin Ashera da yake kusa da shi, duk an sare, bijimi na biyu kuma aka miƙa hadaya a kan sabon bagaden!
Lorsque les gens de la ville se levèrent le lendemain matin, voici que l’autel de Baal était renversé, que l’aschéra qui était auprès était coupée, et que le second taureau était offert en holocauste sur l’autel récemment bâti.
29 Sai suka tambayi junansu, “Wa ya yi wannan?” Sa’ad da suka bincika a hankali, sai aka faɗa musu, “Gideyon ɗan Yowash ne ya yi haka.”
Ils se dirent l’un à l’autre: « Qui a fait cela? » et ils s’informèrent et firent des recherches. On leur dit: « C’est Gédéon, fils de Joas, qui a fait cela. »
30 Mutanen garin suka ce wa Yowash, “Ka kawo mana ɗanka. Dole yă mutu, domin ya rushe bagaden Ba’al, ya sare ginshiƙin Asheran da yake tsaye kusa da shi.”
Alors les gens de la ville dirent à Joas: « Fais sortir ton fils et qu’il meure, car il a renversé l’autel de Baal et coupé l’aschéra qui était auprès. »
31 Amma Yowash ya ce wa taron da suka tayar masa, “Za ku yi hamayya domin Ba’al ne? Kuna ƙoƙari ku cece shi ne? Duk wanda ya yi faɗa saboda shi za a kashe shi kafin safe. In lalle Ba’al allah ne, zai kāre kansa sa’ad da wani ya rushe bagadensa.”
Joas dit à tous ceux qui se tenaient là contre lui: « Est-ce à vous de prendre parti pour Baal? Ou bien est-ce à vous de le secourir? Quiconque prendra parti pour Baal sera mis à mort avant demain matin. Si Baal est Dieu, que lui-même prenne en main sa cause, puisqu’on a renversé son autel! »
32 Saboda haka a ranar suka kira Gideyon, “Yerub-Ba’al,” suna cewa, “Bari Ba’al ya yi hamayya da shi,” domin ya rushe bagaden Ba’al.
En ce jour, un donna à Gédéon le nom de Jérobaal, en disant: « Que Baal se défende contre lui, puisqu’il a renversé son autel! »
33 To, dukan Midiyawa, Amalekawa da sauran mutanen gabashi suka haɗa ƙarfi suka ƙetare Urdun suka kafa sansani a Kwarin Yezireyel.
Tout Madian, Amalec et les fils de l’Orient se rassemblèrent et, ayant passé le Jourdain, ils campèrent dans la plaine de Jezraël.
34 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko wa Gideyon, ya kuma busa ƙaho, ya kira mutanen Abiyezer su bi shi.
L’Esprit de Yahweh revêtit Gédéon; il sonna de la trompette, et les Abiésérites s’assemblèrent pour marcher à sa suite.
35 Ya aika manzanni ko’ina a Manasse, yana kiransu su kintsa, haka ma Asher, Zebulun da Naftali, ta haka su ma suka haura su sadu da su.
Il envoya des messagers dans tout Manassé, qui s’assembla aussi pour le suivre. Il envoya des messagers dans Aser, dans Zabulon et dans Nephtali, et ils montèrent à leur rencontre.
36 Gideyon ya cewa Allah, “In za ka ceci Isra’ila ta hannuna yadda ka yi alkawari,
Gédéon dit à Dieu: « Si vous voulez sauver Israël par ma main, comme vous l’avez dit,
37 to, zan shimfiɗa ulu a masussuka, inda safe akwai raɓa a kan ulun kaɗai, ƙasa kuwa a bushe, to, zan san cewa za ka ceci Isra’ila ta hannuna, yadda ka ce.”
voici, je mettrai une toison de laine sur l’aire: si la toison seule se couvre de rosée, et que tout le sol alentour reste sec, je connaîtrai que vous délivrerez Israël par ma main, comme vous l’avez dit. »
38 Abin da faru ke nan. Gideyon ya tashi da sassafe kashegari, ya matse ulun ya kakkaɓe raɓar, ruwan ya cika ƙwarya.
Et il arriva ainsi. Le jour suivant, s’étant levé de bon matin, il pressa la toison, et en fit sortir la rosée, plein une coupe d’eau.
39 Sa’an nan Gideyon ya ce wa Allah, “Kada ka yi fushi da ni. Bari in ƙara yin wani gwaji kuma da ulun. A wannan lokaci ka sa ulun yă bushe, ƙasar kuma ta rufu da raɓa.”
Gédéon dit à Dieu: « Que votre colère ne s’enflamme pas contre moi; que je puisse encore parler une fois: je voudrais une fois encore seulement faire une épreuve avec la toison: que la toison seule reste sèche, et que la rosée tombe sur tout le sol alentour. »
40 A wannan dare Allah ya yi haka. Ulun ne kaɗai yake a bushe, amma dukan ƙasar ta jiƙe da raɓa.
Et Dieu fit ainsi cette nuit-là: la toison seule resta sèche, et tout le sol se couvrit de rosée.

< Mahukunta 6 >