< Mahukunta 21 >
1 Mutanen Isra’ila sun riga sun yi rantsuwa a Mizfa cewa, “Ba ɗayanmu da zai ba da’yarsa aure ga mutumin Benyamin.”
Après cela, les fils d'Israël en Masdepha prêtèrent ce serment: Nul de nous ne donnera sa fille en mariage à un homme de Benjamin.
2 Sai mutanen suka tafi Betel, inda suka zauna a gaban Allah har yamma, suna tā da muryoyinsu suna kuka mai zafi.
Le peuple revint ensuite à Béthel; il y demeura jusqu'au soir devant Dieu, et ils élevèrent la voix, et ils pleurèrent amèrement.
3 Suka ce, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, “Me ya sa wannan abu ya faru da Isra’ila? Don me kabila ɗaya daga Isra’ila za tă ɓace a yau?”
Et ils dirent: Seigneur, pourquoi faut-il que ce malheur soit arrivé, et que l'une des tribus ait été retranchée d'Israël?
4 Kashegari da sassafe mutane suka gina bagade suka miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta salama.
Le jour parut, et le peuple se leva de grand matin, et il bâtit en ce lieu un autel, et il offrit en holocauste des victimes sans tache.
5 Sa’an nan Isra’ilawa suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji ba?” Gama an yi rantsuwa cewa duk wanda ya kāsa zuwa taro a gaban Ubangiji a Mizfa lalle a kashe shi.
Et les fils d'Israël dirent: Qui donc de tout le peuple n'a point paru à l'assemblée devant le Seigneur? Car ils avaient prêté un serment solennel contre ceux qui n'étaient point montés à Massepha devant le Seigneur, disant: Qu'ils soient mis à mort.
6 To, Isra’ilawa suka yi juyayin’yan’uwansu, mutanen Benyamin. “Yau an hallaka kabila daga cikin Isra’ila.
Et les fils d'Israël furent touchés de regret au sujet de Benjamin, leur frère, et ils dirent: L'une des tribus aujourd'hui a été retranchée d'Israël.
7 Yaya za mu ba wa waɗanda suka rage mata, da yake mun riga mun yi rantsuwa a gaban Ubangiji, ba za mu ba su ɗaya daga’ya’yanmu su aura ba?”
Que ferons-nous pour les survivants qui n'ont point de femmes, nous qui avons juré devant le Seigneur de ne point leur donner nos filles en mariage?
8 Sa’an nan suka ce, “Wace kabila ce cikin kabilan Isra’ila ba tă zo taro a gaban Ubangiji a Mizfa ba?” Sai su gane cewa babu wani daga Yabesh Gileyad da ya zo sansani don taron.
Puis, ils dirent: Est-il quelqu'un parmi les tribus d'Israël qui ne soit point venu devant le Seigneur à Massopha? Et on leur déclara qu'il n'était venu au camp personne de Jabes-Galaad.
9 Gama da aka yi ƙidaya mutane, sai aka gane cewa babu wani daga mutanen Yabesh Gileyad da yake a can.
En effet, le peuple fut recensé, et il n'y avait là aucun des habitants de Jabes-Galaad.
10 Saboda haka sai taron ya umarci jarumai dubu goma sha biyu su je Yabesh Gileyad su karkashe waɗanda suke zaune a can, duk da mata da yara.
Aussitôt, la synagogue fit marcher deux mille vaillants hommes contre cette ville, et elle leur donna ses ordres, disant: Allez et passez au fil de l'épée les habitants de Jabes-Galaad.
11 Suka ce musu, “Ga abin da za ku yi. Ku karkashe duk namiji da kowace macen da ta riga ta san namiji.”
Voici ce que vous ferez: Tout homme et toute femme ayant connu la couche d'un homme, vous les anathématiserez; quant aux vierges, vous les réserverez. Et ils firent ainsi.
12 Suka samu a cikin mutanen da suke zaune a Yabesh Gileyad mata ɗari huɗu da ba su taɓa kwana da namiji ba, suka kwashe su zuwa sansani a Shilo a Kan’ana.
Or, ils trouvèrent parmi les habitants de Jabes-Galaad quatre cents vierges qui ne connaissaient ni les hommes, ni la couche des hommes, et ils les amenèrent au camp de Silo, en la terre de Chanaan.
13 Sa’an nan dukan taro suka aika wa mutanen Benyamin da suke a Dutsen Rimmon cewa yaƙi ya ƙare, yanzu sai salama.
Alors, toute la synagogue dépêcha des envoyés qui parlèrent aux fils de Benjamin en la roche de Rhemmon, et ils les appelèrent à un entretien pacifique.
14 Saboda haka mutanen Benyamin suka komo a lokacin aka kuma ba su matan Yabesh Gileyad nan da aka bari da rai. Amma matan ba su ishe su duka ba.
En ce temps-là, Benjamin revint aux fils d'Israël, et les fils d'Israël leur donnèrent en mariage les filles qu'ils avaient épargnées en Jabes-Galaad. Et ils l'eurent pour agréable.
15 Mutanen kuwa suka yi juyayi saboda mutanen Benyamin, domin Ubangiji ya yi gibi a cikin kabilan Isra’ila.
Cependant le peuple fut encore touché de regrets au sujet de Benjamin, parce que le Seigneur avait retranché l'une des tribus d'Israël.
16 Shugabannin taron suka ce, “Da matan Benyamin da aka hallaka, yaya za mu yi da mazan da suka ragu da ba su sami mata ba?”
Et les anciens de l'assemblée dirent: Que ferons-nous pour que les survivants aient des femmes? Toutes les femmes de Benjamin avaient péri.
17 Suka ce, “Dole mutanen Benyamin da suka ragu su sami gādo, domin kada wata kabila a Isra’ila ta ɓace.
Les anciens dirent encore: Que l'héritage reste à ceux de Benjamin qui survivent, et l'une des tribus d'Israël ne sera point effacée;
18 Ba za mu iya ba su’yan matanmu su zama matansu ba, da yake mu Isra’ilawa mun riga mun yi wannan rantsuwa cewa, ‘La’ananne ne wanda ya ba da’yarsa aure ga mutum Benyamin.’
Mais, nous ne pouvons leur accorder en mariage nos filles, puis qu'entre nous nous avons juré, disant: Maudit celui qui mariera sa fille à Benjamin.
19 Sai suka tuna, akwai bikin Ubangiji da sukan yi shekara-shekara a Shilo ya yi kusa. Shilo yana arewancin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.”
Ils ajoutèrent: C'est bientôt la fête du Seigneur que l'on a célébrée d'âge en âge à Silo (cette ville est au nord de Béthel, à l'orient du chemin qui monte de Béthel à Sichem et au midi de Lebona).
20 Saboda haka suka cewa mutanen Benyamin, “Ku je ku ɓuya a gonakin inabi
Puis, ils donnèrent leurs instructions aux fils de Benjamin, disant: Allez et cachez-vous dans les vignes.
21 ku lura. Sa’ad da’yan matan Shilo suka fito waje don su yi rawa, ku fito a guje daga gonakin inabi, kowannenku yă kama wa kansa mata daga cikin’yan matan Shilo, ku tafi ƙasar Benyamin.
Vous observerez, et, quand vous verrez les filles des habitants de Silo sortir pour former des chœurs de danses, sortez aussi des vignes et enlevez chacun l'une des filles de Silo; emmenez-la en Benjamin.
22 Sa’ad da iyayensu maza ko’yan’uwansu suka kawo mana ƙara, za mu ce musu, ‘Ku yi mana alheri ku bar su, domin ba mu samo musu mata ba lokacin yaƙi, ku kuma marasa laifi ne, tun da yake ba ku ba da’ya’yan matanku gare su ba.’”
Et, lorsque leurs pères ou leurs frères viendront nous demander justice, nous leur dirons pour vous: Faites miséricorde; nul de nous n'a pu prendre femme dans le combat; vous-mêmes ne nous en avez point donné; c'est de votre part qu'est la faute.
23 Haka mutanen Benyamin suka yi. Yayinda’yan matan suke rawa, kowane mutum ya kama ɗaya ya yi gaba da ita ta zama matarsa. Sa’an nan suka komo ƙasar gādonsu suka sāke giggina garuruwan suka kuwa zauna a cikinsu.
Les fils de Benjamin agirent ainsi; ils prirent autant de femmes qu'ils étaient d'hommes, parmi celles qui dansaient; après les avoir ravies, ils les emmenèrent, et ils retournèrent en leur héritage, ou ils rebâtirent leurs villes et ils demeurèrent.
24 A lokacin, Isra’ilawa sun bar wurin suka tafi gida zuwa ga kabilansu da zuriyoyinsu, kowane zuwa gādonsa.
Les fils d'Israël en temps-là se dispersèrent, et chacun rentra dans sa tribu, dans sa famille, dans son héritage.
25 A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa ya yi abin da ya ga dama.
Et, en ces jours-là, il n'y avait point de roi en Israël; chacun faisait ce que bon lui semblait.