< Mahukunta 14 >
1 Samson ya gangara zuwa Timna a can ya ga wata daga cikin’yan mata Filistiyawa.
Šel pak Samson do Tamnata, a uzřel tam ženu ze dcer Filistinských.
2 Da ya komo, sai ya gaya wa mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, “Na ga wata mace a Timna; ku auro mini ita ta zama matata.”
A navrátiv se, oznámil otci svému a mateři své, řka: Viděl jsem ženu v Tamnata ze dcer Filistinských, protož nyní vezměte mi ji za manželku.
3 Mahaifinsa da mahaifiyarsa suka ce, “Babu wata karɓaɓɓiyar yarinya a cikin zuriyarku ko cikin dukan mutanenmu ne? Dole ne ka tafi wajen Filistiyawa marasa kaciya ka nemi aure?” Amma Samson ya ce wa mahaifinsa, “A auro mini ita dai. Ita ta dace da ni.”
I řekl mu otec jeho a matka jeho: Zdali není mezi dcerami bratří tvých a ve všem lidu mém ženy, že sobě vzíti chceš manželku z Filistinských neobřezaných? Odpověděl Samson otci svému: Tuto vezměte mi, nebť mi se líbí.
4 (Iyayensa ba su san cewa wannan daga wurin Ubangiji ne ba, wanda yake neman hanyar da za a kai wa Filistiyawa hari; gama a lokacin suna mulkin Isra’ila.)
Otec pak jeho a matka jeho nevěděli, by to od Hospodina bylo, a že příčiny hledá od Filistinských; nebo toho času panovali Filistinští nad Izraelem.
5 Sai Samson ya gangara zuwa Timna tare da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa. Da suka yi kusa da gonar inabin Timna, nan da nan sai ga ɗan zaki ya taso ya nufe shi yana ruri.
Tedy šel Samson a otec jeho i matka jeho do Tamnata. Když pak přišli k vinicím Tamnatským, a aj, lev mladý řvoucí potkal se s ním.
6 Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko masa da ƙarfi, ya sa ya yaga zakin kashi biyu da hannu kamar yadda akan yayyage ɗan akuya. Sai dai bai gaya wa iyayensa abin da ya yi ba.
I sstoupil na něj Duch Hospodinův, a roztrhl lva, jako by roztrhl kozelce, ačkoli nic neměl v rukou svých. A neoznámil otci ani mateři své, co učinil.
7 Sa’an nan ya gangara ya yi magana da yarinyar, yana kuwa sonsa.
Přišed tedy, mluvil s ženou tou, a líbila se Samsonovi.
8 Daga baya, da ya koma don yă aure ta, sai ya ratse don yă ga gawar zakin. Sai ga taron ƙudan zuma da zuma a ciki,
Navracuje se pak po několika dnech, aby ji pojal, uchýlil se, aby pohleděl na mrtvého lva, a aj, v těle jeho byl roj včel a med.
9 wanda ya sa hannu ya ɗebo yana tafiya yana sha. Sa’ad da ya iso wurin iyayensa, ya ba su zuman, su ma suka sha. Sai dai bai gaya musu cewa ya ɗebo zuman daga gawar zaki ba.
A vybrav jej na ruce své, šel cestou a jedl; a přišed k otci svému a mateři své, dal jim, i jedli. Ale nepověděl jim, že z mrtvého lva vyňal ten med.
10 To, mahaifinsa ya gangara don yă ga yarinyar. Samson kuwa ya shirya wata liyafa a can, yadda yake bisa ga al’adar angwaye.
Tedy šel otec jeho k ženě té, a učinil tam Samson hody, nebo tak činívali mládenci.
11 Sa’ad da ya bayyana, sai aka haɗa shi abokai talatin.
Když pak jej viděli tam, vybrali z sebe třidceti tovaryšů, aby byli při něm.
12 Sai Samson ya ce, “Bari in yi muku kacici-kacici, in kun ba ni amsa cikin kwana bakwai na wannan biki, zan ba ku riguna lilin talatin da kuma tufafi talatin.
I řekl jim Samson: Vydám vám pohádku, kterouž jestliže mi právě vysvětlíte za sedm dní těchto hodů a uhodnete, dám vám třidceti čechlů a třidcatero roucho proměnné.
13 In kuma ba ku iya ba ni amsar ba, dole ku ba ni rigunan lilin talatin da tufafi talatin.” Suka ce, “Ka gaya mana kacici-kacicin.”
Jestliže mi pak nebudete moci uhodnouti, dáte vy mně třidceti čechlů a třidcatero roucho proměnné. Kteříž odpověděli jemu: Vydej pohádku svou, ať ji slyšíme.
14 Sai ya ce, “Daga mai ci, abinci ya fito; daga mai ƙarfi, abu mai zaki ya fito.” Har kwana uku ba su iya ba da amsa ba.
I řekl jim: Z zžírajícího vyšel pokrm, a z silného vyšla sladkost. I nemohli uhodnouti pohádky té za tři dni.
15 A rana ta huɗu suka ce wa matar Samson “Ki rarrashi mijinki yă bayyana mana kacici-kacicin, ko kuwa mu ƙone ki da gidan mahaifinki duka da wuta. Kun kira mu domin ku yi mana fashi ne?”
Stalo se pak dne sedmého, (nebo byli řekli ženě Samsonově: Namluv muže svého, ať nám vyloží tu pohádku, ať nespálíme tě i domu otce tvého ohněm. Proto-liž, abyste našeho statku dostali, pozvali jste nás? Èi co?
16 Sa’an nan matar Samson ta kwanta masa a jiki tana kuka tana cewa, “Kai maƙiyina ne, lalle ba ka ƙaunata, ka yi wa mutanena kacici-kacici, amma ba ka gaya mini amsar ba.” Ya amsa ya ce, “Ban ma bayyana wa mahaifina ko mahaifiyata ba, to, don me zan bayyana miki?”
I plakala žena Samsonova na něj, řkuci: Jistě nenávidíš mne a nemiluješ mne; pohádku jsi vydal synům lidu mého, a mně jí nechceš povědíti. Kterýž řekl jí: Hle, otci mému a mateři neoznámil jsem, a tobě mám povědíti?
17 Ta yi ta kuka har kwana bakwai na bikin. Saboda haka a rana ta bakwai sai ya gaya mata, don ta dame shi. Ita kuwa ta bayyana kacici-kacicin wa mutanenta.
I plakala na něj do sedmého dne, v nichž měli hody). Dne tedy sedmého pověděl jí, nebo trápila jej; kterážto oznámila pohádku synům lidu svého.
18 Kafin rana ta fāɗi a rana ta bakwai mutane garin suka ce masa, “Me ya fi zuma zaki? Me ya fi zaki ƙarfi?” Samson ya ce musu, “Da ba don kun haɗa baki da matata ba, da ba za ku san amsar kacici-kacici ba.”
Muži tedy města toho dne sedmého, prvé než slunce zapadlo, řekli jemu: Co sladšího nad med, a co silnějšího nad lva? Kterýž řekl jim: Byste byli neorali mou jalovičkou, neuhodli byste pohádky mé.
19 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko masa da iko. Sai ya fita ya gangara zuwa Ashkelon, ya kashe mutanensu talatin, ya kwashe kayansu ya kuma ba da rigunarsu ga waɗanda suka bayyana kacici-kacicin. Cike da fushi, ya haura zuwa gidan mahaifinsa.
I sstoupil na něj Duch Hospodinův, a šel do Aškalon, a pobil z nich třidceti mužů. A vzav loupeže jejich, dal šaty proměnné těm, jenž uhodli pohádku, a rozhněvav se velmi, odšel do domu otce svého.
20 Aka kuma ɗauki matar Samson aka ba wa ɗaya daga cikin waɗanda suka yi masa hidima a bikin.
Žena pak Samsonova dostala se jednomu z tovaryšů jeho, kteréhož on byl k sobě připojil.