< Mahukunta 11 >

1 Yefta mutumin Gileyad, jarumi ne ƙwarai. Mahaifinsa ne Gileyad; mahaifiyar kuwa karuwa ce.
Jephté, le Galaadite, était un vaillant guerrier. Il était fils d'une courtisane et c'est Galaad qui avait engendré Jephté.
2 Matar Gileyad ta haifa masa’ya’ya maza, kuma sa’ad da suka yi girma, sai suka kore Yefta, suka ce “Ba ka da gādo a cikin iyalinmu, domin kai ɗan wata mace ce.”
La femme de Galaad lui enfanta des fils, et les fils de cette femme grandirent et chassèrent Jephté, en lui disant: " Tu n'hériteras pas dans la maison de notre père, car tu es fils d'une autre femme. "
3 Saboda haka Yefta ya tsere daga’yan’uwansa ya zauna a ƙasar Tob, inda waɗansu’yan iska suka kewaye shi suka bi shi.
Et Jephté s'enfuit loin de ses frères, et il habita dans le pays de Tob. Des gens de rien se rassemblèrent autour de Jephté, et ils faisaient avec lui des excursions.
4 Ana nan, sa’ad da Ammonawa suka kai wa Isra’ilawa hari,
Quelque temps après, les fils d'Ammon firent la guerre à Israël.
5 dattawan Gileyad suka je suka nemo Yefta daga ƙasar Tob.
Pendant que les fils d'Ammon faisaient la guerre à Israël, les anciens de Galaad allèrent chercher Jephté au pays de Tob.
6 Suka ce masa, “Ka zo ka zama mana shugaba, don mu yaƙi Ammonawa.”
Ils dirent à Jephté: " Viens, tu seras notre général, et nous combattrons les fils d'Ammon. "
7 Yefta ya ce musu, “Ba kun ƙi ni kuka kuma kore ni daga gidan mahaifina ba? Me ya sa kuke zuwa wurina yanzu sa’ad da kuke cikin wahala?”
Jephté dit aux anciens de Galaad: " Ne m'avez-vous pas haï et chassé de la maison de mon père? Pourquoi venez-vous à moi, maintenant que vous êtes dans la détresse? "
8 Mutanen Gileyad suka ce masa, “Duk da haka, muna juyo wajenka yanzu, ka zo tare da mu mu yaƙi Ammonawa, za ka kuma zama shugaban duk wanda yake zama a Gileyad.”
Les anciens de Galaad dirent à Jephté: " C'est à cause de cela que nous revenons à toi maintenant, pour que tu marches avec nous, que tu combattes les fils d'Ammon, et que tu sois notre chef, le chef de tous les habitants de Galaad. "
9 Yefta ya ce, “A ce kun dawo da ni in yaƙi Ammonawa, Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuna, zan zama shugabanku?”
Jephté répondit aux anciens de Galaad: " Si vous me ramenez pour combattre les fils d'Ammon, et que Yahweh les livre entre mes mains, je serai votre chef. "
10 Dattawan Gileyad suka ce, “Ubangiji ne shaidanmu; za mu yi duk abin da ka ce.”
Les anciens de Galaad dirent à Jephté: " Que Yahweh soit témoin entre nous: nous ferons certainement ce que tu dis. "
11 Saboda haka Yefta ya tafi tare da dattawan Gileyad, mutanen kuwa suka naɗa shi shugabansu da kuma sarkinsu. Ya kuwa maimaita dukan maganarsa a gaban Ubangiji a Mizfa.
Et Jephté partit avec les anciens de Galaad. Le peuple l'établit sur lui pour chef et général, et Jephté répéta toutes ses paroles devant Yahweh à Maspha.
12 Sa’an nan Yefta ya aiki jakadu zuwa wurin sarkin Ammonawa su tambaya, “Me ya haɗa ka da ni, da ka kawo wa ƙasata yaƙi?”
Jephté envoya des messagers au roi des fils d'Ammon, pour lui dire: " Qu'y a-t-il entre moi et toi, que tu sois venu contre moi pour faire la guerre à mon pays? "
13 Sarkin Ammonawa ya ce wa jakadu, “Sa’ad da Isra’ilawa suka fito daga Masar, sun ƙwace mini ƙasa tun daga Arnon zuwa Yabbok, har zuwa Urdun. Yanzu ka mayar mini ita cikin salama.”
Le roi des fils d'Ammon répondit aux messagers de Jephté: " C'est qu'Israël, lorsqu'il monta d'Egypte, s'empara de mon pays, depuis l'Arnon jusqu'au Jaboc et au Jourdain. Rends-le maintenant de bon gré. "
14 Yefta ya sāke aikan jakadu wurin sarki,
Jephté envoya de nouveau des messagers au roi des fils d'Ammon,
15 yana cewa, “Ga abin da Yefta yake faɗi, Isra’ila ba tă ƙwace ƙasar Mowab ko ta Ammonawa ba.
et il lui dit: " Ainsi parle Jephté: Israël ne s'est emparé ni du pays de Moab, ni du pays des fils d'Ammon.
16 Amma sa’ad da suka bar Masar, Isra’ila ta bi ta hamada zuwa Jan Teku har suka zo Kadesh.
Car lorsqu'Israël monta d'Egypte, il marcha dans le désert jusqu'à la mer Rouge, et il arriva à Cadès.
17 Sa’an nan Isra’ila ta aiki jakadu zuwa ga sarkin Edom cewa, ‘Ka ba mu izini mu ratsa ƙasarka,’ amma sarkin Edom bai saurara ba. Suka kuma aika wa sarkin Mowab, shi ma ya ƙi. Saboda haka Isra’ila ta zauna a Kadesh.
Alors Israël envoya des messagers au roi d'Edom, pour lui dire: Laisse-moi, je te prie, passer par ton pays; mais le roi d'Edom n'y consentit pas. Il en envoya aussi au roi de Moab, qui refusa également; et Israël resta à Cadés.
18 “Daga can suka ci gaba ta hamada, suka zaga ƙasashen Edom da Mowab, suka wuce ta gabashin ƙasar Mowab, sa’an nan suka yi sansani a ɗaya gefen Arnon. Ba su shiga yankin Mowab ba, gama Arnon ce iyakarta.
Puis, marchant par le désert, il tourna le pays d'Edom et le pays de Moab, et arriva à l'orient du pays de Moab. Et ils campèrent au delà de l'Arnon, et ils ne vinrent pas sur la frontière de Moab, car l'Arnon est la frontière de Moab.
19 “Sa’an nan Isra’ila ta aiki jakadu zuwa ga Sihon sarkin Amoriyawa, wanda yake mulki a Heshbon, ta ce masa, ‘Ka bar mu mu ratsa ƙasarka mu wuce zuwa wurinmu.’
De là, Israël envoya des messagers à Séhon, roi des Amorrhéens, roi de Hésebon; et Israël lui dit: Laisse-nous, je te prie, passer par ton pays jusqu'à notre lieu.
20 Sihon dai, bai amince da Isra’ila su ratsa ƙasarsa ba. Ya tattara dukan mutanensa suka yi sansani a Yahza suka kuwa yaƙi Isra’ila.
Mais Séhon ne se fia pas assez à Israël pour le laisser passer sur son territoire. Séhon rassembla tout son peuple; ils campèrent à Jasa, et il combattit contre Israël.
21 “Sa’an nan Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya ba da Sihon da dukan mutanensa a hannun Isra’ila, suka kuwa ci nasara a kansu. Isra’ila ta ƙwace dukan ƙasar Amoriyawa da suke zaune a ƙasar,
Et Yahweh, le Dieu d'Israël, livra Séhon et tout son peuple entre les mains d'Israël, qui les battit; et Israël s'empara de tout le pays des Amorrhéens qui habitaient dans cette contrée;
22 suka ƙwace dukan yankin Amoriyawa tun daga ƙasar Arnon zuwa Yabbok, daga hamada har zuwa Urdun.
ils s'emparèrent de tout le territoire des Amorrhéens, depuis l'Arnon jusqu'au Jaboc, et depuis le désert jusqu'au Jourdain.
23 “To, da yake Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya kori Amoriyawa a gaban mutanensa Isra’ila, wane’yanci kake da shi da za ka karɓe ta?
Maintenant que Yahweh, le Dieu d'Israël, a chassé les Amorrhéens devant son peuple d'Israël, toi tu chasserais celui-ci!
24 Ba za ka karɓi abin da allahnka Kemosh ya ba ka ba? Haka mu ma, duk abin da Ubangiji Allahnmu ya riga ya ba mu, za mu mallake shi.
Ce dont ton Dieu Chamos t'a mis en possession, ne le possèdes-tu pas? Et tout ce que Yahweh, notre Dieu, a mis devant nous en notre possession, nous ne le posséderions pas!
25 Ka fi Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab ne? Ka taɓa ji ya yi hamayya da Isra’ila ko yă yi yaƙi da su?
Vaudrais-tu donc mieux que Balac, fils de Séphor, roi de Moab? A-t-il contesté avec Israël, ou lui a-t-il fait la guerre?
26 Shekara ɗari uku Isra’ilawa suka yi zamansu a Heshbon, Arower da ƙauyukan kewayenta da dukan biranen da suke gefen Arnon. Me ya sa ba ka karɓe su a lokacin ba?
Voilà trois cents ans qu'Israël habite à Hésebon et dans les villes de sa dépendance, à Aroër et dans les villes de sa dépendance, ainsi que dans toutes les villes qui sont sur les bords de l'Arnon; pourquoi ne les lui avez-vous pas enlevées pendant ce temps-là?
27 Ban yi maka laifi ba, amma kana musguna mini ta wurin kawo mini hari. Bari Ubangiji yă zama Alƙali, yă yanke hukunci tsakani Isra’ilawa da Ammonawa.”
Moi, je n'ai pas péché contre toi; mais toi, tu agis mal envers moi en me faisant la guerre. Que Yahweh, le Juge suprême, juge aujourd'hui entre les enfants d'Israël et les fils d'Ammon. "
28 Duk da haka sarkin Ammonawa bai kula da saƙon da Yefta ya aika ba.
Le roi des fils d'Ammon, n'écouta pas les paroles que Jephté lui avait envoyé dire.
29 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko wa Yefta. Sai ya haye Gileyad da Manasse, ya ratsa ta Mizfa zuwa Gileyad, daga can kuma ya kai wa Ammonawa hari.
L'Esprit de Yahweh fut sur Jephté. Il traversa Galaad et Manassé, et passa jusqu'à Maspha de Galaad; et de Maspha de Galaad il marcha contre les fils d'Ammon.
30 Yefta kuwa ya yi wa’adi da Ubangiji ya ce, “In ka ba da Ammonawa a hannuwana,
Jephté fit un vœu à Yahweh, en disant:
31 duk abin da ya fara fitowa daga ƙofar gidana don yă tarye ni, sa’ad da na komo daga yaƙi da Ammonawa, zai zama na Ubangiji, zan miƙa shi hadaya ta ƙonawa.”
" Si vous livrez entre mes mains les fils d'Ammon, celui qui sortira des portes de ma maison à ma rencontre, quand je reviendrai heureusement de chez les fils d'Ammon, sera à Yahweh, et je l'offrirai en holocauste. "
32 Sa’an nan Yefta ya haye zuwa wajen Ammonawa don yaƙi da su. Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuwansa.
Jephté s'avança contre les fils d'Ammon, et Yahweh les livra entre ses mains.
33 Ya hallaka birane ashirin tun daga Arower zuwa yankin Minnit, har zuwa Abel-Keramim. Haka Isra’ila ta cinye Ammonawa ƙaf.
Il les battit depuis Aroër jusque vers Mennith, leur prenant vingt villes, et jusqu'à Abel-Keramin; ce fut une très grande défaite. Et les fils d'Ammon furent abaissés devant les enfants d'Israël.
34 Sa’ad da Yefta ya komo gida a Mizfa, wa ya fito yă tarye shi,’yarsa tilo, tana rawa kiɗin ganguna! Ita ce kaɗai’yarsa. Ban da ita ba shi da ɗa ko’ya.
Jephté remonta dans sa maison à Maspha; et voici que sa fille sortit à sa rencontre avec des tambourins et des danses. C'était son unique enfant; hors d'elle, il n'avait ni fils ni fille.
35 Da ya gan ta, sai ya yayyage tufafinsa ya yi kuka ya ce, “Kaito!’Yata! Kin karya mini gwiwa, kuma na lalace, domin na yi wa’adi ga Ubangiji da ba zan iya in karya ba.”
Dès qu'il la vit, il déchira ses vêtements et dit: " Ah! ma fille, tu me renverses et tu es parmi ceux qui me troublent. J'ai ouvert ma bouche à Yahweh, et je ne puis revenir en arrière. "
36 Ta ce, “Mahaifina, idan ka riga ka yi wa Ubangiji magana, sai ka yi da ni yadda ka yi alkawari, da yake Ubangiji ya ɗau maka fansa a kan Ammonawa.”
Elle lui dit: " Mon père, tu as ouvert ta bouche à Yahweh; fais-moi selon ce qui est sorti de ta bouche, puisque Yahweh t'a vengé de tes ennemis, les fils d'Ammon. "
37 Sai ta kuma ce, “Sai dai, ka biya mini wannan bukata guda. Ka ba ni wata biyu in yi ta yawo da ni da ƙawayena a kan duwatsu mu yi makoki, domin ba zan yi aure ba.”
Et elle dit à son père: " Que cette grâce seulement me soit accordée; laisse-moi libre pendant deux mois; je m'en irai, je descendrai pour aller sur les montagnes, et je pleurerai ma virginité avec mes compagnes. "
38 Ya ce mata, “Ki tafi,” Ya bar ta tă tafi har wata biyu. Ita da’yan matan suka tafi a kan duwatsu suka yi ta makoki domin ba za tă taɓa aure ba.
Il répondit: " Va, " et il la laissa aller pour deux mois. Elle s'en alla, elle et ses compagnes, et elle pleura sa virginité sur les montagnes.
39 Bayan watanni biyu ɗin sai ta komo wurin mahaifinta ya kuwa yi da ita yadda ya yi wa’adi. Ita kuwa ba tă taɓa san namiji ba. Wannan ya zama al’ada a Isra’ila,
Les deux mois écoulés, elle revint vers son père, et il accomplit à son égard le vœu qu'il avait fait; et elle n'avait pas connu d'homme. De là vint cette coutume en Israël:
40 cewa kowace shekara’yan mata sukan fita kwana huɗu don yin bikin tunawa da’yar Yefta mutumin Gileyad.
chaque année les filles d'Israël vont célébrer la fille de Jephté, le Galaadite, quatre jours par an.

< Mahukunta 11 >