< Mahukunta 11 >

1 Yefta mutumin Gileyad, jarumi ne ƙwarai. Mahaifinsa ne Gileyad; mahaifiyar kuwa karuwa ce.
Now Jephthah the Gileadite was a mighty man of valor, and he was the son of a prostitute. And Gilead became the father of Jephthah.
2 Matar Gileyad ta haifa masa’ya’ya maza, kuma sa’ad da suka yi girma, sai suka kore Yefta, suka ce “Ba ka da gādo a cikin iyalinmu, domin kai ɗan wata mace ce.”
Gilead's wife bore him sons; and when his wife's sons grew up, they drove out Jephthah, and said to him, "You shall not inherit in our father's house; for you are the son of another woman."
3 Saboda haka Yefta ya tsere daga’yan’uwansa ya zauna a ƙasar Tob, inda waɗansu’yan iska suka kewaye shi suka bi shi.
Then Jephthah fled from his brothers, and lived in the land of Tob: and there were gathered vain fellows to Jephthah, and they went out with him.
4 Ana nan, sa’ad da Ammonawa suka kai wa Isra’ilawa hari,
It happened after a while, that the people of Ammon made war against Israel.
5 dattawan Gileyad suka je suka nemo Yefta daga ƙasar Tob.
It was so, that when the people of Ammon made war against Israel, the elders of Gilead went to get Jephthah out of the land of Tob;
6 Suka ce masa, “Ka zo ka zama mana shugaba, don mu yaƙi Ammonawa.”
and they said to Jephthah, "Come and be our chief, that we may fight with the people of Ammon."
7 Yefta ya ce musu, “Ba kun ƙi ni kuka kuma kore ni daga gidan mahaifina ba? Me ya sa kuke zuwa wurina yanzu sa’ad da kuke cikin wahala?”
And Jephthah said to the elders of Gilead, "Did you not hate me, and drive me out of my father's house, and sent me away from you? And why have you come to me now when you are in distress?"
8 Mutanen Gileyad suka ce masa, “Duk da haka, muna juyo wajenka yanzu, ka zo tare da mu mu yaƙi Ammonawa, za ka kuma zama shugaban duk wanda yake zama a Gileyad.”
The elders of Gilead said to Jephthah, "Not so. We have turned to you now, that you may go with us, and fight with the people of Ammon; and you shall be our head over all the inhabitants of Gilead."
9 Yefta ya ce, “A ce kun dawo da ni in yaƙi Ammonawa, Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuna, zan zama shugabanku?”
Jephthah said to the elders of Gilead, "If you bring me home again to fight with the people of Ammon, and Jehovah delivers them before me, shall I be your head?"
10 Dattawan Gileyad suka ce, “Ubangiji ne shaidanmu; za mu yi duk abin da ka ce.”
The elders of Gilead said to Jephthah, "Jehovah shall be witness between us; surely according to your word so will we do."
11 Saboda haka Yefta ya tafi tare da dattawan Gileyad, mutanen kuwa suka naɗa shi shugabansu da kuma sarkinsu. Ya kuwa maimaita dukan maganarsa a gaban Ubangiji a Mizfa.
Then Jephthah went with the elders of Gilead, and the people made him head and chief over them. And Jephthah spoke all his words before Jehovah in Mizpah.
12 Sa’an nan Yefta ya aiki jakadu zuwa wurin sarkin Ammonawa su tambaya, “Me ya haɗa ka da ni, da ka kawo wa ƙasata yaƙi?”
Jephthah sent messengers to the king of the people of Ammon, saying, "What have you to do with me, that you have come to me to fight against my land?"
13 Sarkin Ammonawa ya ce wa jakadu, “Sa’ad da Isra’ilawa suka fito daga Masar, sun ƙwace mini ƙasa tun daga Arnon zuwa Yabbok, har zuwa Urdun. Yanzu ka mayar mini ita cikin salama.”
And the king of the people of Ammon answered the messengers of Jephthah, "Because Israel took away my land, when he came up out of Egypt, from the Arnon even to the Jabbok, and to the Jordan. Now therefore restore it peaceably, and I will depart."
14 Yefta ya sāke aikan jakadu wurin sarki,
And the messengers returned to Jephthah, and Jephthah sent messengers again to the king of the people of Ammon;
15 yana cewa, “Ga abin da Yefta yake faɗi, Isra’ila ba tă ƙwace ƙasar Mowab ko ta Ammonawa ba.
and he said to him, "Thus says Jephthah: 'Israel did not take away the land of Moab, nor the land of the people of Ammon,
16 Amma sa’ad da suka bar Masar, Isra’ila ta bi ta hamada zuwa Jan Teku har suka zo Kadesh.
but when they came up from Egypt, and Israel went through the wilderness to the Red Sea, and came to Kadesh;
17 Sa’an nan Isra’ila ta aiki jakadu zuwa ga sarkin Edom cewa, ‘Ka ba mu izini mu ratsa ƙasarka,’ amma sarkin Edom bai saurara ba. Suka kuma aika wa sarkin Mowab, shi ma ya ƙi. Saboda haka Isra’ila ta zauna a Kadesh.
then Israel sent messengers to the king of Edom, saying, 'Please let me pass through your land.' But the king of Edom did not listen. In the same way, he sent to the king of Moab; but he would not. So Israel stayed in Kadesh.
18 “Daga can suka ci gaba ta hamada, suka zaga ƙasashen Edom da Mowab, suka wuce ta gabashin ƙasar Mowab, sa’an nan suka yi sansani a ɗaya gefen Arnon. Ba su shiga yankin Mowab ba, gama Arnon ce iyakarta.
Then they went through the wilderness, and went around the land of Edom, and the land of Moab, and came by the east side of the land of Moab, and they camped on the other side of the Arnon; but they did not come within the territory of Moab, for the Arnon was the boundary of Moab.
19 “Sa’an nan Isra’ila ta aiki jakadu zuwa ga Sihon sarkin Amoriyawa, wanda yake mulki a Heshbon, ta ce masa, ‘Ka bar mu mu ratsa ƙasarka mu wuce zuwa wurinmu.’
Israel sent messengers to Sihon king of the Amorites, the king of Heshbon; and Israel said to him, "Please let me pass through your land to our land.'
20 Sihon dai, bai amince da Isra’ila su ratsa ƙasarsa ba. Ya tattara dukan mutanensa suka yi sansani a Yahza suka kuwa yaƙi Isra’ila.
But Sihon did not trust Israel to pass through his territory; but Sihon gathered all his people together, and camped in Jahaz, and fought against Israel.
21 “Sa’an nan Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya ba da Sihon da dukan mutanensa a hannun Isra’ila, suka kuwa ci nasara a kansu. Isra’ila ta ƙwace dukan ƙasar Amoriyawa da suke zaune a ƙasar,
Jehovah, the God of Israel, delivered Sihon and all his people into the hand of Israel, and they struck them. So Israel possessed all the land of the Amorites, the inhabitants of that country.
22 suka ƙwace dukan yankin Amoriyawa tun daga ƙasar Arnon zuwa Yabbok, daga hamada har zuwa Urdun.
They possessed all the territory of the Amorites, from the Arnon even to the Jabbok, and from the wilderness even to the Jordan.
23 “To, da yake Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya kori Amoriyawa a gaban mutanensa Isra’ila, wane’yanci kake da shi da za ka karɓe ta?
So now Jehovah, the God of Israel, has driven out the Amorites from before his people Israel, and should you possess them?
24 Ba za ka karɓi abin da allahnka Kemosh ya ba ka ba? Haka mu ma, duk abin da Ubangiji Allahnmu ya riga ya ba mu, za mu mallake shi.
Won't you possess that which Chemosh your god gives you to possess? So whoever Jehovah our God has driven out from before us, we will possess.
25 Ka fi Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab ne? Ka taɓa ji ya yi hamayya da Isra’ila ko yă yi yaƙi da su?
And now are you anything better than Balak the son of Zippor, king of Moab? Did he ever contend against Israel, or did he ever fight against them?
26 Shekara ɗari uku Isra’ilawa suka yi zamansu a Heshbon, Arower da ƙauyukan kewayenta da dukan biranen da suke gefen Arnon. Me ya sa ba ka karɓe su a lokacin ba?
While Israel lived in Heshbon and its towns, and in Aroer and its towns, and in all the cities that are along by the side of the Arnon, three hundred years; why did you not liberate them within that time?
27 Ban yi maka laifi ba, amma kana musguna mini ta wurin kawo mini hari. Bari Ubangiji yă zama Alƙali, yă yanke hukunci tsakani Isra’ilawa da Ammonawa.”
I therefore have not sinned against you, but you do me wrong by making war against me. Jehovah, the Judge, be judge this day between the children of Israel and the people of Ammon."
28 Duk da haka sarkin Ammonawa bai kula da saƙon da Yefta ya aika ba.
However the king of the people of Ammon did not listen to the words of Jephthah which he sent him.
29 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko wa Yefta. Sai ya haye Gileyad da Manasse, ya ratsa ta Mizfa zuwa Gileyad, daga can kuma ya kai wa Ammonawa hari.
Then the Spirit of Jehovah came on Jephthah, and he passed over Gilead and Manasseh, and passed over Mizpeh of Gilead, and from Mizpeh of Gilead he passed over to the people of Ammon.
30 Yefta kuwa ya yi wa’adi da Ubangiji ya ce, “In ka ba da Ammonawa a hannuwana,
Jephthah made a vow to Jehovah, and said, "If you will indeed deliver the people of Ammon into my hand,
31 duk abin da ya fara fitowa daga ƙofar gidana don yă tarye ni, sa’ad da na komo daga yaƙi da Ammonawa, zai zama na Ubangiji, zan miƙa shi hadaya ta ƙonawa.”
then it shall be that whatever comes forth from the doors of my house to meet me, when I return in peace from the people of Ammon, it shall be Jehovah's, and I will offer it up for a burnt offering."
32 Sa’an nan Yefta ya haye zuwa wajen Ammonawa don yaƙi da su. Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuwansa.
So Jephthah passed over to the people of Ammon to fight against them; and Jehovah delivered them into his hand.
33 Ya hallaka birane ashirin tun daga Arower zuwa yankin Minnit, har zuwa Abel-Keramim. Haka Isra’ila ta cinye Ammonawa ƙaf.
He struck them from Aroer until you come to Minnith, even twenty cities, and to Abel Keramim, with a very great slaughter. So the people of Ammon were subdued before the children of Israel.
34 Sa’ad da Yefta ya komo gida a Mizfa, wa ya fito yă tarye shi,’yarsa tilo, tana rawa kiɗin ganguna! Ita ce kaɗai’yarsa. Ban da ita ba shi da ɗa ko’ya.
Jephthah came to Mizpah to his house; and look, his daughter came out to meet him with tambourines and with dances: and she was his only child; besides her he had neither son nor daughter.
35 Da ya gan ta, sai ya yayyage tufafinsa ya yi kuka ya ce, “Kaito!’Yata! Kin karya mini gwiwa, kuma na lalace, domin na yi wa’adi ga Ubangiji da ba zan iya in karya ba.”
And it happened, when he saw her, that he tore his clothes, and said, "Alas, my daughter. You have brought me very low. You have become a stumbling block in my sight. And you are among those who trouble me. For I have given my word to Jehovah, and I can't break it."
36 Ta ce, “Mahaifina, idan ka riga ka yi wa Ubangiji magana, sai ka yi da ni yadda ka yi alkawari, da yake Ubangiji ya ɗau maka fansa a kan Ammonawa.”
She said to him, "My father, since you have given your word to Jehovah; do to me as you promised, because Jehovah has taken vengeance for you on your enemies, even on the people of Ammon."
37 Sai ta kuma ce, “Sai dai, ka biya mini wannan bukata guda. Ka ba ni wata biyu in yi ta yawo da ni da ƙawayena a kan duwatsu mu yi makoki, domin ba zan yi aure ba.”
She said to her father, "Let this thing be done for me: leave me alone two months, that I may depart and go down on the mountains, and weep because of my virginity, I and my companions."
38 Ya ce mata, “Ki tafi,” Ya bar ta tă tafi har wata biyu. Ita da’yan matan suka tafi a kan duwatsu suka yi ta makoki domin ba za tă taɓa aure ba.
He said, "Go." He sent her away for two months: and she departed, she and her companions, and wept because of her virginity on the mountains.
39 Bayan watanni biyu ɗin sai ta komo wurin mahaifinta ya kuwa yi da ita yadda ya yi wa’adi. Ita kuwa ba tă taɓa san namiji ba. Wannan ya zama al’ada a Isra’ila,
It happened at the end of two months, that she returned to her father, who did with her according to what he had vowed. And she was a virgin. It became a custom in Israel,
40 cewa kowace shekara’yan mata sukan fita kwana huɗu don yin bikin tunawa da’yar Yefta mutumin Gileyad.
that the daughters of Israel went yearly four days in a year to commemorate the daughter of Jephthah the Gileadite.

< Mahukunta 11 >