< Yoshuwa 1 >

1 Bayan mutuwar Musa bawan Ubangiji, sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa ɗan Nun, mataimakin Musa,
Und es geschah nach dem Tode Moses, des Knechtes Jehovahs, daß Jehovah zu Joschua, dem Sohne Nuns, Moses Diener, sprach und sagte:
2 “Bawana Musa ya mutu. Yanzu sai ka tashi tare da mutanen nan duka, ku yi shirin ƙetare kogin Urdun zuwa cikin ƙasar da zan ba su Isra’ilawa.
Mose, mein Knecht, ist tot, und nun mache du dich auf, gehe über diesen Jordan, du und all dies Volk, nach dem Lande, das Ich ihnen, den Söhnen Israels gebe.
3 Zan ba ku duk ƙasar da za ku taka, kamar yadda na yi wa Musa alkawari.
Jeder Ort, darauf eure Fußsohle tritt, habe Ich euch gegeben, wie Ich zu Mose geredet habe.
4 Ƙasar da ta kama daga hamada zuwa Lebanon, zuwa babban Kogin, wato, Kogin Yuferites, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum, wajen yamma.
Von der Wüste und diesem Libanon und bis zu dem großen Flusse, dem Flusse Euphrat, alles Land der Chethiter und bis zum großen Meer, zum Untergang der Sonne, soll eure Grenze sein.
5 Ba wanda zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai; ba zan taɓa rabuwa da kai ba; ba zan yashe ka ba.
Kein Mensch soll bestehen vor dir alle Tage deines Lebens. Wie Ich mit Mose war, will Ich mit dir sein, und dich nicht aufgeben, noch dich verlassen.
6 “Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, gama kai za ka bi da mutanen nan har su karɓi ƙasar da na yi wa kakanninsu alkawari zan ba su.
Sei stark und rüstig; denn du sollst diesem Volk das Land, das Ich ihren Vätern geschworen habe, ihnen zu geben, als Erbe austeilen.
7 Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, ka yi lura fa, ka yi biyayya da dokokin da bawana Musa ya ba ka; kada ka kauce ga bin dokokin ko hagu ko dama, domin ka yi nasara a duk, inda za ka je.
Sei nur stark und sehr rüstig, daß du haltest zu tun nach all dem Gesetz, das dir Mose, Mein Knecht, geboten hat. Weiche nicht ab davon, weder zur Rechten, noch zur Linken, auf daß du klüglich handelst überall, wo du hingehst.
8 Kada ka bar Littafin Dokokin nan yă rabu da bakinka, sai dai ka yi ta tunani game da shi dare da rana, don ka lura, ka yi duk abin da aka rubuta a ciki, ta haka ne za ka yi nasara cikin duk abin da za ka yi.
Laß dieses Gesetzbuch nicht von deinem Munde weichen und sinne darüber Tag und Nacht, auf daß du haltest zu tun nach allem, das darin geschrieben ist; denn dann gelingt dir es auf deinem Wege, und dann handelst du klüglich.
9 Ba ni na umarce ka ba? Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro. Kada ka ji tsoro; kada ka karaya, gama Ubangiji Allahnka zai kasance tare da kai duk inda za ka je.”
Habe Ich dir nicht geboten, du sollest stark sein und rüstig, sollst kein Grauen und kein Entsetzen haben?, denn Jehovah, dein Gott, ist mit dir, überall wo du hingehst.
10 Saboda haka sai Yoshuwa ya umarci shugabannin mutane,
Und Joschua gebot den Vorstehern des Volkes und sprach:
11 “Ku ratsa cikin sansani, ku gaya wa mutane, ‘Ku shirya guzurinku. Nan da kwana uku za ku ƙetare Urdun a nan, don ku je ka mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ta zama taku.’”
Gehet hin mitten durch das Lager und gebietet dem Volke und sprechet: Bereitet euch Zehrung; denn in noch drei Tagen ziehet ihr über diesen Jordan, daß ihr hineinkommt und das Land einnehmet, das Jehovah, euer Gott, euch zum Erbbesitze gibt.
12 Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse,
Und zu den Rubeniten und den Gaditern und zu dem halben Stamm Menascheh sprach Joschua und sagte:
13 “Ku tuna da umarnin da Musa bawan Ubangiji ya yi muku. ‘Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa, ya kuma ba ku wannan ƙasa.’
Gedenket des Wortes, das euch Mose, der Knecht Jehovahs, geboten hat und gesagt: Jehovah, euer Gott, hat euch zur Ruhe gebracht und euch dies Land gegeben;
14 Matanku, da yaranku, da kuma dabbobinku za su kasance a ƙasar da Musa ya ba ku a gabashin Urdun, amma dole mayaƙanku, su yi shirin yaƙi su haye, su yi gaba tare da’yan’uwanku, za ku taimaki’yan’uwanku
Eure Weiber, eure Kindlein und eure Viehherden dürfen in dem Lande bleiben, das euch Mose diesseits des Jordans gegeben hat. Ihr aber sollt kampfgerüstet vor euren Brüdern hinüberziehen, alle tapferen Männer, und sollt ihnen beistehen.
15 har sai lokacin da Ubangiji ya ba su hutawa, kamar yadda ya yi muku, kuma har sai su ma sun ƙwace ƙasar da Ubangiji Allahnku ya yi alkawari zai ba su. Bayan haka ne za ku koma ku mallaki ƙasarku, wadda Musa bawan Ubangiji ya ba ku a gabashin Urdun.”
Bis daß Jehovah eure Brüder wie euch zur Ruhe gebracht hat, und auch sie das Land eingenommen haben, das Jehovah, euer Gott, ihnen gibt. Dann dürft ihr in das Land eures Erbbesitzes zurückkehren und dasselbe erblich besitzen, das euch Mose, der Knecht Jehovahs, diesseits des Jordans gegen Aufgang der Sonne gegeben hat.
16 Sai suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “Duk abin da ka ce mu yi, za mu yi. Duk inda kuma ka aike mu, za mu je.
Und sie antworteten Joschua und sprachen: Alles, was du uns geboten hast, wollen wir tun, und wohin du uns sendest, wollen wir gehen.
17 Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya, haka za mu yi maka biyayya. Ubangiji Allahnka ya kasance tare da Musa.
Ganz so, wie wir auf Mose hörten, so werden wir auf dich hören. Nur möge Jehovah, dein Gott, mit dir sein, wie Er mit Mose gewesen ist.
18 Duk wanda ya yi wa maganarka tawaye, ya ƙi yă yi biyayya da maganarka, ko da umarnin da ka ba shi, za a kashe shi. Ka dai ƙarfafa ka kuma yi ƙarfi hali!”
Jeder Mann, der deinem Mund widerspenstig ist und nicht hört auf deine Worte in allem, das du uns gebietest, der soll getötet werden. Nur sei stark und rüstig.

< Yoshuwa 1 >