< Yoshuwa 9 >
1 To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
All the kings west of the Jordan heard what had happened. These included the kings of the Hittites, Amorites, Canaanites, Perizzites, Hivites, and Jebusites who lived in the hill country, the lowlands, and along the coast as far as Lebanon.
2 suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
So they gathered to fight together as a united army against Joshua and the Israelites.
3 Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
But when the people of Gibeon heard what Joshua had done to Jericho and Ai,
4 sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
they decided on a cunning plan. They sent messengers to Joshua, their donkeys wearing worn-out saddles and carrying old wineskins that were torn and patched.
5 Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
They put on worn sandals that had been mended and wore old clothes. All their bread was dry and moldy.
6 Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
They went to Joshua at the camp in Gilgal and told him and the men of Israel, “We have come from a land far away, so please make a treaty with us.”
7 Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
But the Israelites said to the Hivites, “Maybe you live close by. If you do, we cannot make a treaty with you.”
8 Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
“We are your servants,” they replied. “But who are you? Where do you come from?” Joshua asked.
9 Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
“Your servants have come from a land far away,” they replied. “For we have heard of the reputation of the Lord your God, and reports of all that he did in Egypt,
10 da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
and what he did to the two Amorite kings east of the Jordan—to Sihon, king of Heshbon, and Og, king of Bashan, who ruled in Ashtaroth.
11 Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
So our leaders and everyone who lives in our land told us: Take what you need with you for the journey. Go and meet with them, and tell them, ‘We are your servants. Please make a treaty with us.’
12 Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
Look at this bread. It was warm when we took it from our houses on the day we set out to come here. But now it's dry and moldy, as you can see.
13 Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
These wineskins were new when we filled them, but look at them now—they're split and damaged. These clothes of ours and our sandals are all worn out because the journey took so long.”
14 Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
The Israelites tried some of the food. However, they did not consult the Lord.
15 Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
Then Joshua made a treaty with them, promising to spare their lives, and the leaders of the assembly swore an oath to guarantee it.
16 Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
Three days after they had made the treaty, the Israelites learned that the Gibeonites lived nearby, right among them!
17 Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
The Israelites left to go to the Gibeonite towns, and arrived there on the third day. The towns were Gibeon, Kephirah, Beeroth and Kiriath Jearim.
18 Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
But the Israelites did not attack them because of the treaty sworn by the leaders of the assembly in the name of the Lord, the God of Israel. At this all the Israelites protested against the leaders.
19 Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
But the leaders replied to the people, “We swore to them by the Lord, the God of Israel, so we cannot lay a hand on them now.
20 Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
So this is what we're going to do to them. We'll let them live, so that we won't be punished for breaking the oath that we swore to them.”
21 Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
The leaders concluded, “Let them live.” So the Gibeonites became woodcutters and water-carriers in service to the entire assembly, as the Israelite leaders had ordered.
22 Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
Then Joshua summoned the Gibeonites and asked them, “Why did you trick us? You told us, ‘We live a long way from you,’ but you live right next door to us!
23 Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
Consequently you are under a curse. From now on you shall forever be servants, woodcutters and water-carriers for the house of my God.”
24 Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
They answered Joshua, “We your servants were told very clearly that the Lord your God had ordered Moses to give you all this land, and that all its inhabitants were to be wiped out before you. So we really feared for our lives because of you. That's why we did what we did.
25 Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
Now we're in your hands. Do to us what you think is right and just.”
26 Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
Joshua did as he had said. He saved them from the Israelites, so that they did not kill them.
27 A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.
That day Joshua made them woodcutters and water-carriers in service to the entire assembly and for the altar of the Lord wherever the Lord should choose. That is what they do right up to this very day.