< Yoshuwa 9 >

1 To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
Da alle Kongerne på den anden Side af Jordan, i Bjergene og i Lavlandet og langs hele det store Havs Kyst hen imod Libanon, Hetiterne, Amoriterne, Kana'anæerne, Perizziterne, Hivviterne og Jebusiterne, hørte, hvad der var sket,
2 suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
samlede de sig for i Fællesskab at kæmpe mod Josua og Israel.
3 Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
Men da Indbyggerne i Gibeon hørte, hvad Josua havde gjort ved Jeriko og Aj,
4 sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
greb også de til en List; de gik hen og forsynede sig med Rejsetæring, læssede nogle slidte Sække og nogle slidte, sprukne, stoppede Vinsække på deres Æsler
5 Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
og tog slidte, lappede Sko på Fødderne og slidte Klæder på Kroppen, og alt deres Rejsebrød var tørt og mullent.
6 Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
Så gik de til Josua i Lejren ved Gilgal og sagde til ham og Israels Mænd: "Vi kommer fra et fjernt Land; slut derfor Pagt med os!"
7 Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
Israels Mænd svarede Hivviterne: "Det kunde være, at I bor her midt iblandt os, hvorledes kan vi da slutte Pagt med eder?"
8 Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
De sagde til Josua: "Vi er dine Trælle!" Josua spurgte dem så: "Hvem er I, og hvorfra kommer I?"
9 Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
Og de svarede ham: "Fra et såre fjernt Land er dine Trælle kommet for HERREN din Guds Navns Skyld; thi vi har hørt hans Ry og alt, hvad han gjorde i Ægypten,
10 da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
og alt, hvad han gjorde mod de to Amoriterkonger hinsides Jordan, Kong Sihon af Hesjbon og Kong Og af Basan, som boede i Asjtarot.
11 Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
og vore Ældste og alle Indbyggerne i vort Land sagde til os: Tag Rejse tæring med eder, drag dem i Møde og sig til dem: Vi er eders Trælle; slut derfor nu Pagt med os!
12 Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
Vort Brød her var endnu varmt, da vi tog det med hjemmefra, dengang vi begav os af Sted for at drage til eder; men se, nu er det tørt og mullent;
13 Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
og vore Vinsække her var nye, da vi fyldte dem; se, nu er de sprukne; og vore Klæder og Sko her er slidte, fordi Vejen var så lang!"
14 Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
Så tog Mændene af deres Rejsetæring; men HERREN rådspurgte de ikke.
15 Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
Og Josua tilsagde dem Fred og sluttede Overenskomst med dem og lovede at lade dem leve, og Menighedens Øverster tilsvor dem det.
16 Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
Men tre Dage efter at de havde sluttet Pagt med dem, hørte de, at de var fra den nærmeste Omegn og boede midt iblandt dem.
17 Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
Og Israeliterne brød op og kom den tredje Dag til deres Byer, det var Gibeon, Kefira, Beerot og Kirjat Jearim.
18 Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
Men Israeliterne dræbte dem ikke, fordi Menighedens Øverster havde, tilsvoret dem Fred ved HERREN, Israels Gud. Da knurrede hele Menigheden mod Øversterne;
19 Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
men alle Øversterne sagde til hele Menigheden: "Vi har tilsvoret dem Fred ved HERREN, Israels Gud, derfor kan vi ikke gøre dem noget ondt.
20 Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
Men dette vil vi gøre med dem, når vi skåner deres Liv, at der ikke skal komme Vrede over os for den Ed, vi svor dem:
21 Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
De skal blive i Live, men være Brændehuggere og Vandbærere for hele Menigheden." Og hele Menigheden gjorde, som Øverstene havde sagt.
22 Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
Og Josua lod dem kalde og talte således til dem: "Hvorfor førte I os bag Lyset og sagde, at I havde hjemme langt borte fra os, skønt I bor her midt iblandt os?
23 Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
Derfor skal I nu være forbandede, og ingen af eder skal nogen Sinde ophøre at være Træl; Brændehuggere og Vandbærere skal I være ved min Gus Hus!"
24 Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
De svarede Josua og sagde:"Det var blevet dine Trælle sagt, at HERREN din Gud pålagde sin Tjener Moses, at når han gav eder hele Landet, skulde I udrydde alle Landets Indbyggere foran eder. Da påkom der os stor Frygt for, at I skulde tage vort Liv; derfor handlede vi således.
25 Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
Men se, nu er vi i din Hånd; gør med os, som det tykkes dig godt og ret!"
26 Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
Da handlede han således med dem; han friede dem fra Israeliternes Hånd, så de ikke dræbte dem;
27 A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.
men Josua gjorde dem den Dag til Brændehuggere og Vandbærere for Menigheden og for HERRENs Alter på det Sted, han vilde udvælge. Og det er de den Dag i Dag.

< Yoshuwa 9 >