< Yoshuwa 23 >

1 An daɗe bayan da Ubangiji ya ba Isra’ilawa hutu daga dukan abokan gāban da suke kewaye da su. Yoshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa,
Og det skete mange Aar efter, at Herren havde skaffet Israel Rolighed for alle deres Fjender trindt omkring, og Josva var gammel, var kommen til Aars:
2 sai ya aika a kira Isra’ilawa duka, dattawansu, shugabanninsu, alƙalansu, da manyan ma’aikatansu, ya ce musu, “Na tsufa, shekaruna kuwa sun yi yawa,
Da kaldte Josva ad alt Israel, ad deres Ældste og deres Øverster og deres Dommere og deres Fogeder, og han sagde til dem: Jeg er gammel, jeg er kommen til Aars.
3 ku kanku kun ga dukan abubuwan da Ubangiji Allahnku ya yi da idanunku wa dukan ƙasashen nan, Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku.
Og I have set alt, hvad Herren eders Gud har gjort ved alle disse Folk for eders Ansigt; thi Herren eders Gud, han er den, som har stridt for eder.
4 Ku tuna yadda na rarraba wa kabilanku ƙasashen nan su zama naku na gādo, dukan ƙasashen da suka rage, ƙasashen da na ci da yaƙi, tsakanin Urdun da Bahar Rum a yamma.
Ser, jeg har ladet disse Folk, som ere overblevne, tilfalde eder til Arv for eders Stammer, fra Jordanen af, tillige med alle de Folk, som jeg har udryddet, og indtil det store Hav mod Solens Nedgang.
5 Ubangiji Allahnku kansa zai kore su a madadinku. Zai fafare su a gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu, yadda Ubangiji Allah ya yi muku alkawari.
Og Herren eders Gud, han skal udstøde dem fra eders Ansigt, og han skal fordrive dem fra at være for eders Ansigt; og I skulle eje deres Land, som Herren eders Gud har tilsagt eder.
6 “Ku yi ƙarfin hali, ku yi hankali, ku yi biyayya da dukan abin da aka rubuta a cikin Littafin Dokoki na Musa, ba tare da kun juya hagu ko dama ba.
Saa værer saare stærke til at holde og at gøre alt det, som er skrevet i Mose Lovbog, saa at I ikke vige derfra til højre eller venstre Side,
7 Kada ku haɗa kai da mutanen nan da suke zama cikinku; ba ruwanku da sunayen allolinsu, kada ku rantse da su. Kada kuwa ku bauta musu ko kuwa ku rusuna musu.
at I ikke komme iblandt disse Folk, som ere tilovers hos eder, og I ikke nævne eller lade sværge ved deres Guders Navn og ikke tjene dem og ikke tilbede dem;
8 Sai dai ku riƙe Ubangiji Allahnku da kyau, yadda kuka yi har zuwa yanzu.
men I skulle hænge fast ved Herren eders Gud, som I have gjort indtil denne Dag;
9 “Ubangiji ya kori manyan ƙasashe masu ƙarfi; har wa yau ba wanda ya iya cin ku da yaƙi.
thi Herren har fordrevet store og stærke Folk fra eders Ansigt; og ingen har bestaaet for eders Ansigt indtil denne Dag.
10 Mutum ɗaya a cikinku ya isa yă sa mutane dubu nasu su gudu, domin Ubangiji Allahnku yana yaƙi dominku, kamar yadda ya yi alkawari.
Een Mand af eder skal forfølge tusinde; thi Herren eders Gud, han er den, som strider for eder, som han har tilsagt Eder.
11 Saboda haka sai ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku.
Derfor tager nøje Vare paa eders Sjæle, at I elske Herren, eders Gud.
12 “Amma in kuka juya baya kuka zama abokai ga waɗanda suka ragu suke zama a cikinku a ƙasashen nan, har kuka yi auratayya da su, kuka haɗa kai da su,
Thi dersom I vende eder bort og hænge ved disse øvrige Hedninger, disse, som ere tilovers hos eder, og I gøre Svogerskab med dem, og I komme iblandt dem, og de iblandt eder:
13 ku tabbata cewa Ubangiji Allahnku ba zai kore muku mutanen ƙasashen nan ba, sai ma su zama muku dutsen tuntuɓe da tarko, za su zama bulala a bayanku, ƙayayyuwa a idanunku, har sai kun hallaka daga wannan ƙasa mai kyau wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku.
Da skulle I visseligen vide, at Herren eders Gud skal ikke ydermere fordrive disse Folk fra eders Ansigt; men de skulle blive eder til en Fælde og til en Snare og til en Svøbe paa eders Sider og til Brodde i eders Øjne, indtil I omkomme af dette gode Land, som Herren eders Gud har givet eder.
14 “Yanzu na kusa barin fuskar duniyan nan. Kun sani da dukan zuciyarku, da dukan ranku cewa, Ba ko ɗaya daga cikin alkawuran da Ubangiji Allahnku ya yi, da bai cika ba. Kowane alkawari ya cika; ba ko ɗaya da bai cika ba.
Og se, jeg gaar i Dag al Jordens Gang; og I skulle vide i eders ganske Hjerte og i eders ganske Sjæl, at ikke eet Ord er faldet af alle de gode Ord, som Herren eders Gud har talet over eder, at de jo alle ere opfyldte for eder, der faldt ikke et Ord af dem.
15 Kamar yadda Ubangiji Allahnku kuwa ya cika kowane alkawari mai kyau, haka ma ba zai fasa kawo muku bala’in da ya faɗi ba, sai ya hallaka ku daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba ku.
Og det skal ske, at ligesom alle de gode Ord ere opfyldte over eder, som Herren eders Gud har talet til eder, saaledes skal Herren lade alle de onde Ord opfyldes over eder, indtil han udrydder eder af dette gode Land, som Herren eders Gud gav eder.
16 In kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku wanda ya umarce ku, in kuka je kuka bauta wa waɗansu alloli, kuka rusuna musu, fushin Ubangiji zai sauko a kanku, za ku kuwa hallaka da sauri daga ƙasan nan mai kyau da ya ba ku.”
Naar I overtræde Herrens, eders Guds Pagt, som han bød eder, og gaa og tjene andre Guder og tilbede dem, da skal Herrens Vrede optændes imod eder, og I skulle snart omkomme af det gode Land, som han har givet eder.

< Yoshuwa 23 >