< Yoshuwa 17 >

1 Wannan shi ne gādon da aka ba wa kabilar Manasse, a matsayin ɗan farin Yusuf. Manasse yana da ɗan farin mai suna Makir. Makir shi ne mahaifin mutanen Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan gama Makiriyawa jarumai ne ƙwarai.
Forsothe lot felde in to the lynage of Manasse, for he is the firste gendrid sone of Joseph; lot felde to Machir, the firste gendrid sone of Manasses, to the fadir of Galaad, that was a werriour, and he hadde possessioun Galaad and Basan.
2 Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manasse rabon gādonsu bisa ga iyalansu, wato, Abiyezer, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer da Shemida. Waɗannan su ne’ya’yan Manasse, maza, ɗan Yusuf bisa ga iyalansu.
And lot felde to the othere of the sones of Manasses, bi her meynees; to the sones of Abiezer, and to the sones of Heleth, and to the sones of Hesriel, and to the sones of Sichen, and to the sones of Epher, and to the sones of Semyda; these ben the sones of Manasse, sone of Joseph, the male children, bi her meynees.
3 Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse ba shi da’ya’ya maza, sai dai mata. Ga sunayensu, Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.
Sotheli to Salphaat, the sone of Epher, sone of Galaad, sone of Machir, sone of Manasses, weren not sones, but douytris aloone; of whiche these ben the names, Maala, and Noa, and Eegla, and Melcha, and Thersa.
4 Suka je wurin Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin, suka ce musu, “Ubangiji ya umarci Musa cewa yă ba mu gādonmu tare da’yan’uwanmu maza.” Saboda haka Yoshuwa ya ba su gādo tare da’yan’uwan mahaifinsu maza bisa ga umarnin Ubangiji.
And thei camen in the siyt of Eleazar, preest, and of Josue, sone of Nun, and of the princes, and seiden, The Lord comaundide bi the hond of Moises, that possessioun should be youun to vs in the myddis of oure britheren. And Josue yaf to hem possessioun, bi comaundement of the Lord, in the myddis of the britheren of her fadir.
5 Dalilin ke nan Manasse ya sami kashi goma ban da ƙasar Gileyad da Bashan a gabashin Urdun,
And ten cordis, `that is, londis mesurid bi ten cordis, felden to Manasses, without the lond of Galaad and of Basan biyende Jordan;
6 domin’ya’ya mata na kabilar Manasse sun sami gādo tare da’ya’ya maza. Aka ba wa sauran mutanen kabilar Manasse ƙasar Gileyad.
for the douytris of Manasses weldiden eritage in the myddis of the sones of hym. Sotheli the lond of Galaad felde in to the part of the sones of Manasses, that weren residue.
7 Iyakar ƙasar Manasse ta tashi daga Asher zuwa Mikmetat a gabashin Shekem. Iyakar kuma ta miƙe har zuwa kudu wadda ta ƙunshi mutanen da suke zaune a En Taffuwa.
And the terme of Manasses was fro Azer Machynathath, that biholdeth Sichem, and goith out to the riyt side, bisidis the dwelleris of the welle Taphue;
8 (Manasse ne yake da ƙasar Taffuwa, amma garin Taffuwa kansa, a kan iyakar Manasse ta mutanen Efraim ce.)
for the lond of Thaphue, which is bisidis the terme of Manasses, and of the sones of Effraym, felde in the lot of Manasses.
9 Sa’an nan iyakar ta ci gaba ta yi kudu zuwa Rafin Kana. Akwai garuruwan da suke kudancin rafin, waɗanda suke Efraim, ko da yake suna cikin yankin Manasse. Iyakar Manasse ta miƙe zuwa arewa ta bi gefen rafin ta kuma ƙarasa a Bahar Rum.
And the terme of the valey of place of rehedis goith doun in the south of the stronde of the citees of Effraym, that ben in the myddis of the citees of Manasses. The terme of Manasses is fro the north of the stronde, and the goyng out therof goith to the see;
10 Ƙasar a wajen kudu ta Efraim ce, ta wajen arewa kuma ta Manasse ce. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Asher yana wajen arewa, Issakar kuma a wajen gabas.
so that the possessioun of Effraym is fro the south, and the possessioun of Manasses fro the north, and the see closith euer either; and tho ben ioyned to hem silf in the linage of Aser fro the north, and in the lynage of Isachar fro the eest.
11 A yanki tsakanin Issakar da Asher, Manasse yana da waɗannan wurare, Bet-Sheyan, Ibileyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan En Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta (Na uku cikin jerin shi ne Nafot).
And the eritage of Manasses was in Isachar and in Aser, Bersan, and the townes therof, and Jeblaan, with hise townes, and the dwellers of Dor, with her citees; and the dwelleris of Endor, with her townes, and also the dwelleris of Thanath, with her townes, and the dwelleris of Maiedo, with her townes, and the thridde part of the citee Nophet.
12 Duk da haka mutanen Manasse ba su iya mallakar garuruwan nan ba, domin Kan’aniyawa sun nace da zama a wannan yanki.
And the sones of Manasses miyten not distrie these citees, but Cananei bigan to dwelle in this lond.
13 Da Isra’ilawa suka yi ƙarfi, sai suka sa Kan’aniyawa suka zama masu yin musu aiki, amma ba su iya korarsu duka ba.
Sotheli aftir that the sones of Israel weren stronge, thei maden suget Cananeis, and maden tributaries to hem silf, and killiden not Cananeis.
14 Mutanen Yusuf kuwa suka ce wa Yoshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo ɗaya kawai? Ga shi muna da yawa kuma Ubangiji ya albarkace mu sosai.”
And the sones of Joseph spaken to Josue, and seiden, Whi hast thou youe to me lond in to possessioun of o lot and part, sithen Y am of so greet multitude, and the Lord hath blesside me, `that is, hath alargid me in children?
15 Yoshuwa ya ce musu, “In kuna da yawa sosai, in kuma ƙasar kan tudu ta Efraim ba ta ishe ku ba, sai ku je cikin jeji, ku nema wa kanku ƙasa a ƙasar Ferizziyawa da Refahiyawa.”
To whiche Josue seide, If thou art myche puple, stie thou into the wode, and kitte doun to thee spaces in the lond of Feresei, and of Raphaym, for the possessioun of the hil of Effraym is streiyt to thee.
16 Mutanen Yusuf suka amsa suka ce, “Ƙasar kan tudu ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawan da suke zama a filin, da waɗanda suke Bet-Sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke Kwarin Yezireyel, duk suna da keken yaƙin ƙarfe.”
To whom the sones of Joseph answerden, We moun not stie to the hilli places, sithen Cananeis, that dwellen in the `lond of the feeld, vsen ironne charis; in which lond Bersan, with hise townes, and Jesrael, weldynge the myddil valey, ben set.
17 Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Yusuf, wa Efraim da Manasse, “Kuna da yawa, kuna kuma da ƙarfi sosai. Ba wuri ɗaya kaɗai za ku samu gādo ba,
And Josue seide to the hows of Joseph, and of Effraym, and of Manasses, Thou art myche puple, and of greet strengthe; thou schalt not haue o lot,
18 amma har da ƙasar kan tudu ma, ko da yake jeji ne, ku je ku gyara shi, duk yă zama naku. Ko da yake Kan’aniyawa suna da kekunan yaƙi na ƙarfe, suna kuma da ƙarfi, duk da haka za ku kore su.”
but thou schalt passe to the hil, and thou schalt kitte doun to thee; and thou schalt clense spaces to dwelle. And thou schalt mow go forth ferthere, whanne thou hast distried Cananei, whom thou seist to haue irone charis, and to be moost strong.

< Yoshuwa 17 >