< Yoshuwa 17 >

1 Wannan shi ne gādon da aka ba wa kabilar Manasse, a matsayin ɗan farin Yusuf. Manasse yana da ɗan farin mai suna Makir. Makir shi ne mahaifin mutanen Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan gama Makiriyawa jarumai ne ƙwarai.
And it belonged the lot to [the] tribe of Manasseh for he [was] [the] firstborn of Joseph to Makir [the] firstborn of Manasseh [the] father of Gilead for he he was a man of war and it belonged to him Gilead and Bashan.
2 Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manasse rabon gādonsu bisa ga iyalansu, wato, Abiyezer, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer da Shemida. Waɗannan su ne’ya’yan Manasse, maza, ɗan Yusuf bisa ga iyalansu.
And it belonged to [the] descendants of Manasseh who remained to clans their to [the] descendants of Abiezer and to [the] descendants of Helek and to [the] descendants of Asriel and to [the] descendants of Shechem and to [the] descendants of Hepher and to [the] descendants of Shemida these [were] [the] descendants of Manasseh [the] son of Joseph the males to clans their.
3 Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse ba shi da’ya’ya maza, sai dai mata. Ga sunayensu, Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.
And to Zelophehad [the] son of Hepher [the] son of Gilead [the] son of Makir [the] son of Manasseh not they belonged to him sons that except daughters and these [are] [the] names of daughters his Mahlah and Noah Hoglah Milcah and Tirzah.
4 Suka je wurin Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin, suka ce musu, “Ubangiji ya umarci Musa cewa yă ba mu gādonmu tare da’yan’uwanmu maza.” Saboda haka Yoshuwa ya ba su gādo tare da’yan’uwan mahaifinsu maza bisa ga umarnin Ubangiji.
And they drew near before Eleazar the priest and before - Joshua [the] son of Nun and before the leaders saying Yahweh he commanded Moses to give to us an inheritance in among brothers our and he gave to them to [the] mouth of Yahweh an inheritance in among [the] brothers of father their.
5 Dalilin ke nan Manasse ya sami kashi goma ban da ƙasar Gileyad da Bashan a gabashin Urdun,
And they fell [the] allotted portions of Manasseh ten apart from [the] land of Gilead and Bashan which [is] from [the] other side of the Jordan.
6 domin’ya’ya mata na kabilar Manasse sun sami gādo tare da’ya’ya maza. Aka ba wa sauran mutanen kabilar Manasse ƙasar Gileyad.
For [the] daughters of Manasseh they inherited an inheritance in among sons his and [the] land of Gilead it belonged to [the] descendants of Manasseh who remained.
7 Iyakar ƙasar Manasse ta tashi daga Asher zuwa Mikmetat a gabashin Shekem. Iyakar kuma ta miƙe har zuwa kudu wadda ta ƙunshi mutanen da suke zaune a En Taffuwa.
And it was [the] border of Manasseh from Asher Micmethath which [is] on [the] face of Shechem and it goes the border to the south to [the] inhabitants of En Tappuah.
8 (Manasse ne yake da ƙasar Taffuwa, amma garin Taffuwa kansa, a kan iyakar Manasse ta mutanen Efraim ce.)
To Manasseh it belonged [the] land of Tappuah and Tappuah to [the] border of Manasseh [belonged] to [the] descendants of Ephraim.
9 Sa’an nan iyakar ta ci gaba ta yi kudu zuwa Rafin Kana. Akwai garuruwan da suke kudancin rafin, waɗanda suke Efraim, ko da yake suna cikin yankin Manasse. Iyakar Manasse ta miƙe zuwa arewa ta bi gefen rafin ta kuma ƙarasa a Bahar Rum.
And it goes down the border [the] wadi of Kanah [the] south towards to the wadi cities these [belonged] to Ephraim in among [the] cities of Manasseh and [the] border of Manasseh [was] from [the] north of the wadi and it was extremities its the sea towards.
10 Ƙasar a wajen kudu ta Efraim ce, ta wajen arewa kuma ta Manasse ce. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Asher yana wajen arewa, Issakar kuma a wajen gabas.
South-ward [belonged] to Ephraim and north-ward [belonged] to Manasseh and it was the sea border its and Asher they touch! from [the] north and Issachar from [the] east.
11 A yanki tsakanin Issakar da Asher, Manasse yana da waɗannan wurare, Bet-Sheyan, Ibileyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan En Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta (Na uku cikin jerin shi ne Nafot).
And it belonged to Manasseh in Issachar and in Asher Beth Shean and daughters its and Ibleam and daughters its and [the] inhabitants of Dor and daughters its and [the] inhabitants of En-dor and daughters its and [the] inhabitants of Taanach and daughters its and [the] inhabitants of Megiddo and daughters its [the] three of Napheth.
12 Duk da haka mutanen Manasse ba su iya mallakar garuruwan nan ba, domin Kan’aniyawa sun nace da zama a wannan yanki.
And not they were able [the] descendants of Manasseh to take possession of the cities these and he was determined the Canaanite[s] to dwell in the land this.
13 Da Isra’ilawa suka yi ƙarfi, sai suka sa Kan’aniyawa suka zama masu yin musu aiki, amma ba su iya korarsu duka ba.
And it was that they became strong [the] people of Israel and they made the Canaanite[s] forced labor and certainly not he dispossessed him.
14 Mutanen Yusuf kuwa suka ce wa Yoshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo ɗaya kawai? Ga shi muna da yawa kuma Ubangiji ya albarkace mu sosai.”
And they spoke [the] descendants of Joseph with Joshua saying why? have you given to me an inheritance a lot one and a portion one and I [am] a people numerous to that until thus he has blessed me Yahweh.
15 Yoshuwa ya ce musu, “In kuna da yawa sosai, in kuma ƙasar kan tudu ta Efraim ba ta ishe ku ba, sai ku je cikin jeji, ku nema wa kanku ƙasa a ƙasar Ferizziyawa da Refahiyawa.”
And he said to them Joshua if [are] a people numerous you go up for yourself the forest towards and you will cut down for yourself there in [the] land of the Perizzite[s] and the Rephaites that it is narrow for you [the] hill country of Ephraim.
16 Mutanen Yusuf suka amsa suka ce, “Ƙasar kan tudu ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawan da suke zama a filin, da waɗanda suke Bet-Sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke Kwarin Yezireyel, duk suna da keken yaƙin ƙarfe.”
And they said [the] descendants of Joseph not it will be found for us the hill country and chariotry of iron [is] among all the Canaanite[s] who dwells in [the] land of the valley to [those] who [are] in Beth Shean and daughters its and to [those] who [are] in [the] valley of Jezreel.
17 Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Yusuf, wa Efraim da Manasse, “Kuna da yawa, kuna kuma da ƙarfi sosai. Ba wuri ɗaya kaɗai za ku samu gādo ba,
And he said Joshua to [the] house of Joseph to Ephraim and to Manasseh saying [are] a people numerous you and strength great [belongs] to you not it will belong to you a lot one.
18 amma har da ƙasar kan tudu ma, ko da yake jeji ne, ku je ku gyara shi, duk yă zama naku. Ko da yake Kan’aniyawa suna da kekunan yaƙi na ƙarfe, suna kuma da ƙarfi, duk da haka za ku kore su.”
For [the] hill country it will belong to you for [is] forest it and you will cut down it and it will belong to you extremities its for you will dispossess the Canaanite[s] for chariotry of iron [belongs] to him that [is] strong he.

< Yoshuwa 17 >