< Yoshuwa 15 >

1 An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
La part échue par le sort à la tribu des fils de Juda, selon leurs familles, s’étendait vers la frontière d’Édom, jusqu’au désert de Tsin, au midi, à l’extrémité méridionale.
2 Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
Ainsi, leur limite méridionale partait de l’extrémité de la mer Salée, de la langue qui fait face au sud.
3 zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
Elle se prolongeait au midi de la montée d’Akrabbim, passait par Tsin, et montait au midi de Kadès-Barnéa; elle passait de là par Hetsron, montait vers Addar, et tournait à Karkaa;
4 Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
elle passait ensuite par Atsmon, et continuait jusqu’au torrent d’Égypte, pour aboutir à la mer. Ce sera votre limite au midi.
5 Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
La limite orientale était la mer Salée jusqu’à l’embouchure du Jourdain. La limite septentrionale partait de la langue de mer qui est à l’embouchure du Jourdain.
6 wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
Elle montait vers Beth-Hogla, passait au nord de Beth-Araba, et s’élevait jusqu’à la pierre de Bohan, fils de Ruben;
7 Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
elle montait à Debir, à quelque distance de la vallée d’Acor, et se dirigeait vers le nord du côté de Guilgal, qui est vis-à-vis de la montée d’Adummim au sud du torrent. Elle passait près des eaux d’En-Schémesch, et se prolongeait jusqu’à En-Roguel.
8 Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
Elle montait de là par la vallée de Ben-Hinnom au côté méridional de Jebus, qui est Jérusalem, puis s’élevait jusqu’au sommet de la montagne, qui est devant la vallée de Hinnom à l’occident, et à l’extrémité de la vallée des Rephaïm au nord.
9 Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
Du sommet de la montagne elle s’étendait jusqu’à la source des eaux de Nephthoach, continuait vers les villes de la montagne d’Éphron, et se prolongeait par Baala, qui est Kirjath-Jearim.
10 Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
De Baala elle tournait à l’occident vers la montagne de Séir, traversait le côté septentrional de la montagne de Jearim, à Kesalon, descendait à Beth-Schémesch, et passait par Thimna.
11 Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
Elle continuait sur le côté septentrional d’Ékron, s’étendait vers Schicron, passait par la montagne de Baala, et se prolongeait jusqu’à Jabneel, pour aboutir à la mer.
12 Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
La limite occidentale était la grande mer. Telles furent de tous les côtés les limites des fils de Juda, selon leurs familles.
13 Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
On donna à Caleb, fils de Jephunné, une part au milieu des fils de Juda, comme l’Éternel l’avait ordonné à Josué; on lui donna Kirjath-Arba, qui est Hébron: Arba était le père d’Anak.
14 Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
Caleb en chassa les trois fils d’Anak: Schéschaï, Ahiman et Talmaï, enfants d’Anak.
15 Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
De là il monta contre les habitants de Debir: Debir s’appelait autrefois Kirjath-Sépher.
16 Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
Caleb dit: Je donnerai ma fille Acsa pour femme à celui qui battra Kirjath-Sépher et qui la prendra.
17 Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
Othniel, fils de Kenaz, frère de Caleb, s’en empara; et Caleb lui donna pour femme sa fille Acsa.
18 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
Lorsqu’elle fut entrée chez Othniel, elle le sollicita de demander à son père un champ. Elle descendit de dessus son âne, et Caleb lui dit: Qu’as-tu?
19 Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
Elle répondit: Fais-moi un présent, car tu m’as donné une terre du midi; donne-moi aussi des sources d’eau. Et il lui donna les sources supérieures et les sources inférieures.
20 Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
Tel fut l’héritage des fils de Juda, selon leurs familles.
21 Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
Les villes situées dans la contrée du midi, à l’extrémité de la tribu des fils de Juda, vers la frontière d’Édom, étaient: Kabtseel, Éder, Jagur,
22 Kina, Dimona, Adada,
Kina, Dimona, Adada,
23 Kedesh, Hazor, Itnan,
Kédesch, Hatsor, Ithnan,
24 Zif, Telem, Beyalot,
Ziph, Thélem, Bealoth,
25 Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
Hatsor-Hadattha, Kerijoth-Hetsron, qui est Hatsor,
26 Amam, Shema, Molada,
Amam, Schema, Molada,
27 Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
Hatsar-Gadda, Heschmon, Beth-Paleth,
28 Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
Hatsar-Schual, Beer-Schéba, Bizjothja,
29 Ba’ala, Iyim, Ezem,
Baala, Ijjim, Atsem,
30 Eltolad, Kesil, Horma,
Eltholad, Kesil, Horma,
31 Ziklag, Madmanna, Sansanna,
Tsiklag, Madmanna, Sansanna,
32 Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
Lebaoth, Schilhim, Aïn, et Rimmon. Total des villes: vingt-neuf, et leurs villages.
33 Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
Dans la plaine: Eschthaol, Tsorea, Aschna,
34 Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
Zanoach, En-Gannim, Tappuach, Énam,
35 Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
Jarmuth, Adullam, Soco, Azéka,
36 Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
Schaaraïm, Adithaïm, Guedéra, et Guedérothaïm; quatorze villes, et leurs villages.
37 Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
Tsenan, Hadascha, Migdal-Gad,
38 Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
Dilean, Mitspé, Joktheel,
39 Lakish, Bozkat, Eglon,
Lakis, Botskath, Églon,
40 Kabbon, Lahman, Kitlish,
Cabbon, Lachmas, Kithlisch,
41 Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
Guedéroth, Beth-Dagon, Naama, et Makkéda; seize villes, et leurs villages.
42 Libna, Eter, Ashan,
Libna, Éther, Aschan,
43 Yefta, Ashna, Nezib,
Jiphtach, Aschna, Netsib,
44 Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
Keïla, Aczib, et Maréscha; neuf villes, et leurs villages.
45 Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
Ékron, les villes de son ressort et ses villages;
46 yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
depuis Ékron et à l’occident, toutes les villes près d’Asdod, et leurs villages,
47 Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
Asdod, les villes de son ressort, et ses villages; Gaza, les villes de son ressort, et ses villages, jusqu’au torrent d’Égypte, et à la grande mer, qui sert de limite.
48 Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
Dans la montagne: Schamir, Jatthir, Soco,
49 Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
Danna, Kirjath-Sanna, qui est Debir,
50 Anab, Eshtemo, Anim,
Anab, Eschthemo, Anim,
51 Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
Gosen, Holon, et Guilo, onze villes, et leurs villages.
52 Arab, Duma, Eshan,
Arab, Duma, Eschean,
53 Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
Janum, Beth-Tappuach, Aphéka,
54 Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
Humta, Kirjath-Arba, qui est Hébron, et Tsior; neuf villes, et leurs villages.
55 Mawon, Karmel, Zif, Yutta
Maon, Carmel, Ziph, Juta,
56 Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
Jizreel, Jokdeam, Zanoach,
57 Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
Kaïn, Guibea, et Thimna; dix villes, et leurs villages.
58 Halhul, Bet-Zur, Gedor,
Halhul, Beth-Tsur, Guedor,
59 Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
Maarath, Beth-Anoth, et Elthekon; six villes, et leurs villages.
60 Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
Kirjath-Baal, qui est Kirjath-Jearim, et Rabba; deux villes, et leurs villages.
61 Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
Dans le désert: Beth-Araba, Middin, Secaca,
62 Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
Nibschan, Ir-Hammélach, et En-Guédi; six villes, et leurs villages.
63 Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.
Les fils de Juda ne purent pas chasser les Jébusiens qui habitaient à Jérusalem, et les Jébusiens ont habité avec les fils de Juda à Jérusalem jusqu’à ce jour.

< Yoshuwa 15 >