< Yoshuwa 14 >
1 Ga wuraren da Isra’ilawa suka sami gādo a ƙasar Kan’ana waɗanda Eleyazar firist, Yoshuwa ɗan Nun da kuma shugabannin iyalai kabila-kabila na Isra’ila suka raba musu.
Irezao o linova’ o ana’ Israeleo an-tane Kanàneo, o zinara’ i Eleazare mpisoroñe naho Iehosoa ana’ i None naho o talèn’ anjomban-droaem-pifokoan’ ana’ Israeleo am’ iereo ho fanañañe;
2 Ta wurin yin ƙuri’a aka raba wa kabilan nan tara da rabi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.
an-tsapake ty nahazoañe o lovao, ty amy linili’ Iehovà am-pità’ i Mosèy ho a i fifokoañe sive rey naho i vaki’eiy—
3 Musa ya ba wa kabilan biyu da rabin nan gādonsu gabashin Urdun, amma bai ba wa Lawiyawa gādo a cikin sauran ba,
amy te natolo’ i Mosè ty lova’ i fifokoa roe naho vaki’e rey alafe’ Iardeney añe; fe tsy nanolora’e anjara am’ iareo ao o nte-Levio.
4 gama’ya’yan Yusuf sun zama kabilu biyu, Manasse da Efraim. Ba a ba Lawiyawa gādon ba sai dai garuruwan da aka ba su su zauna a ciki, da wurin kiwo mai kyau domin dabbobinsu.
Roe ‘nio ty fifokoa’ i ana’ Iosefe rey, i Menasè naho i Efraime; vaho tsy nimea’ iareo anjara o nte-Levio naho tsy o rova fimoneña’ iareoo naho ty tane fiandrazañe mañohoke iareo ho amo hare’eo naho ho famahanañe iareo;
5 Haka Isra’ilawa suka raba ƙasar, yadda Ubangiji ya umarci Musa.
ze nandilia’ Iehovà i Mosèy, le nanoe’ o ana’ Israeleo, amy fanjarañe i taneiy.
6 Mutanen Yahuda kuma suka je wurin Yoshuwa a Gilgal, sai Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze ya ce wa Yoshuwa, “Ka san abin da Ubangiji ya gaya wa Musa, mutumin Allah a Kadesh Barneya game da kai da ni.
Nifanontoñe am’ Iehosoa amy zao o ana’ Iehoda e Gilgaleo; le hoe t’i Kalebe ana’ Iefonè nte-Kenize ama’e: Fohi’o i entañe tsinara’ Iehovà amy Mosè ondatin’ Añahare ty amako naho ama’o e Kadese-barnea añey.
7 Ina da shekara arba’in lokacin da Musa bawan Ubangiji ya aike ni zuwa Kadesh Barneya in leƙi asirin ƙasar. Na kuwa kawo masa rahoto daidai yadda na ga ƙasar,
Ni-efa-polo taon-draho te nirahe’ i Mosè mpitoro’ Iehovà boake Kadese-barnea hitampoñe amy taney ao; vaho nimpoly ninday ty entan-troko.
8 amma’yan’uwana waɗanda muka je tare su suka ba da rahoton da ya sa zukatan mutane suka narke don tsoro. Ni kam na bi Ubangiji Allah da dukan zuciyata.
Toe nampitronake ty arofo’ ondatio o rahalahy nindre lia amakoo; fe Iehovà Andrianañahareko avao ty noriheko.
9 Saboda haka a ranan nan Musa ya rantse mini cewa, ‘Ƙasar da ka taka za tă zama ƙasarka ta gādo kai da’ya’yanka har abada, domin ka bi Ubangiji Allahna da dukan zuciyarka.’
Nifanta amy andro zay t’i Mosè, ami’ty hoe: Toe ho lovae’o naho o ana’oo nainai’e o tane liniam-pandia’oo, amy te norihe’o ami’ty halifora’e t’Iehovà Andrianañahareko.
10 “Ga shi, kamar yadda Ubangiji ya yi alkawari, ya bar ni da rai har na ƙara shekaru arba’in da biyar tun daga lokacin da ya gaya wa Musa wannan, a lokacin da Isra’ilawa suke yawo a cikin jeji. Ga ni nan yau shekaruna tamanin da biyar!
Ie amy zao, hehe te nitana’ Iehovà velon-draho, amy tsara’ey, i efa-polo-lim’ amby taoñe boak’ amy andro nitsarà’ Iehovà amy Mosè i entañe zaiy, ie nirererere am-patrambey añe t’Israele; aa le an-taom-balo-polo-lim’ amby iraho henaneo.
11 Ina nan da ƙarfina kamar yadda nake da ƙarfi a lokacin da Musa ya aike ni; zan iya fita zuwa yaƙi da ƙwazo yanzu kamar yadda nake zuwa a dā.
Fe mira amy andro nañiraha’ i Mosè ahiy ty hafatrarako androany; manahake ty haozarako henane zay ty haozarako henane zao, hahafialiako naho hiavotako vaho himoahako.
12 Yanzu sai ka ba ni wannan ƙasar da take kan tudu wadda Ubangiji ya yi alkawari zai ba ni a ranan nan. Kai ma ka ji a lokacin, yadda Anakawa suke a can, biranensu manya ne kuma sun kewaye su sosai, amma na sani Ubangiji zai taimake ni, zan kore su kamar yadda ya faɗa.”
Aa ie henaneo, atoloro ahy ty vohitse toy, i tsinara’ Iehovà amy andro zaiy, ie jinanji’o amy andro zay te ao o nte-Anàkeo, aman-drova jabajaba naho fatratse; hera hañimb’ ahy t’Iehovà vaho ho roaheko, ty amy tsara’ Iehovày.
13 Sai Yoshuwa ya sa wa Kaleb ɗan Yefunne albarka, ya ba shi Hebron.
Aa le tinata’ Iehosoa; vaho natolo’e amy Kalebe ana’ Iefonè ty Kebrone ho lova.
14 Saboda haka Hebron ta zama ƙasar Kaleb ɗan Yefunne Bakenizze tun daga lokacin nan, domin ya bi Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa.
Aa le ninjare lova’ i Kalebe ana’ Iefonè nte-Kenize t’i Kebrone, ampara o andro zao; amy te norihe’e an-kaliforan-troke t’Iehovà Andrianañahare’ Israele.
15 (Dā a kan kira wannan Hebron, Kiriyat Arba. Wannan Arba kuwa shi ne wani katon mutum a cikin Anakawa.) Sa’an nan ƙasar ta huta daga yaƙi.
Kiriate-arbà ty añara’ i Kebrone taolo, fa nifanalolahy amo nte-Anàke iabio t’i Arbà. Nitofa amy aliy i taney henane zay.