< Yoshuwa 12 >

1 Waɗannan su ne sarakunan ƙasashen da Isra’ilawa suka ci da yaƙi, suka kuma mallaki ƙasarsu a gabashin Urdun, daga kwarin Arnon zuwa Dutsen Hermon haɗe da dukan gefen gabas na Araba.
And these [are] kings of the land whom the sons of Israel have struck, and possess their land beyond the Jordan, at the sun-rising, from the Brook of Arnon to Mount Hermon, and all the plain eastward:
2 Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Ya yi mulki daga Arower wadda take iyakar kwarin Arnon, daga tsakiyar kwarin har zuwa, Kogin Yabbok, wanda yake iyakar Ammonawa. Wannan ya haɗa da rabin Gileyad.
Sihon, king of the Amorite, who is dwelling in Heshbon, ruling from Aroer which [is] on the border of the Brook of Arnon, and the middle of the brook, and half of Gilead, and to the Brook of Jabok, the border of the sons of Ammon;
3 Ya kuma yi mulki a kan gabashin Araba daga tekun Kinneret zuwa Tekun Araba (wato, Tekun Gishiri), zuwa Bet-Yeshimot da kuma kudu zuwa gangaren dutsen Fisga.
and the plain to the Sea of Chinneroth eastward, and to the Sea of the Plain (the Salt Sea) eastward, the way to Beth-Jeshimoth, and from the south under the Springs of Pisgah.
4 Haka ma suka ci sashen Og sarkin Bashan, ɗaya daga cikin Refahiyawa na ƙarshe da ya yi mulki a Ashtarot da Edireyi.
And the border of Og king of Bashan (of the remnant of the Rephaim), who is dwelling in Ashtaroth and in Edrei,
5 Mulkinsa ya taso daga Dutsen Hermon, da Saleka, da dukan Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma’akatiyawa haɗe da rabin Gileyad, zuwa kan iyakar Heshbon ta sarki Sihon.
and ruling in Mount Hermon, and in Salcah, and in all Bashan, to the border of the Geshurite, and the Maachathite, and the half of Gilead, the border of Sihon king of Heshbon.
6 Sai Musa, bawan Ubangiji da Isra’ilawa suka ci Sihon da Og da yaƙi. Musa bawan Ubangiji kuwa ya ba da ƙasarsu ga mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse.
Moses, servant of YHWH, and the sons of Israel have struck them, and Moses, servant of YHWH, gives it—a possession to the Reubenite, and to the Gadite, and to the half of the tribe of Manasseh.
7 Waɗannan su ne sarakuna da kuma ƙasashen da Yoshuwa da Isra’ilawa suka ci da yaƙi a yammancin Urdun, daga Ba’al-Gad a Kwarin Lebanon zuwa Dutsen Halak wanda ya miƙe zuwa Seyir. Yoshuwa ya raba ƙasarsu ta zama gādo ga Isra’ilawa bisa ga yadda aka raba su kabila-kabila.
And these [are] kings of the land whom Joshua and the sons of Israel have struck beyond the Jordan westward, from Ba‘al-Gad, in the Valley of Lebanon, and to the Mount of Halak, which is going up to Seir; and Joshua gives it to the tribes of Israel—a possession according to their divisions;
8 Ƙasar ta haɗa da ƙasar kan tudu, filayen arewanci, Araba, gangaren Dutse, da jejin, da kuma Negeb, wato, ƙasashen Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa, da Yebusiyawa.
in the hill-country, and in the low country, and in the plain, and in the springs, and in the wilderness, and in the south; the Hittite, the Amorite, and the Canaanite, the Perizzite, the Hivite, and the Jebusite:
9 Sarkin Yeriko, ɗaya sarkin Ai (kusa da Betel), ɗaya
the king of Jericho, one; the king of Ai, which [is] beside Bethel, one;
10 sarkin Urushalima, ɗaya sarkin Hebron, ɗaya
the king of Jerusalem, one; the king of Hebron, one;
11 sarkin Yarmut, ɗaya sarkin Lakish, ɗaya
the king of Jarmuth, one; the king of Lachish, one;
12 sarkin Eglon, ɗaya sarkin Gezer, ɗaya
the king of Eglon, one; the king of Gezer, one;
13 sarkin Debir, ɗaya sarkin Bet-Gader, ɗaya
the king of Debir, one; the king of Geder, one;
14 sarkin Horma, ɗaya sarkin Arad, ɗaya
the king of Hormah, one; the king of Arad, one;
15 sarkin Libna, ɗaya sarkin Adullam, ɗaya
the king of Libnah, one; the king of Adullam, one;
16 sarkin Makkeda, ɗaya sarkin Betel, ɗaya
the king of Mekkedah, one; the king of Beth-El, one;
17 sarkin Taffuwa, ɗaya sarkin Hefer, ɗaya
the king of Tappuah, one; the king of Hepher, one;
18 sarkin Afek, ɗaya sarkin Sharon, ɗaya
the king of Aphek, one; the king of Lasharon, one;
19 sarkin Madon, ɗaya sarkin Hazor, ɗaya
the king of Madon, one; the king of Hazor, one;
20 sarkin Shimron Meron, ɗaya sarkin Akshaf, ɗaya
the king of Shimron-Meron, one; the king of Achshaph, one;
21 sarkin Ta’anak, ɗaya sarkin Megiddo, ɗaya
the king of Taanach, one; the king of Megiddo, one;
22 sarkin Kedesh, ɗaya sarkin Yokneyam a Karmel, ɗaya
the king of Kedesh, one; the king of Jokneam of Carmel, one;
23 sarkin Dor (A Nafot Dor), ɗaya sarkin Goyim a Gilgal, ɗaya
the king of Dor, at the elevation of Dor, one; the king of the nations of Gilgal, one;
24 sarki Tirza, ɗaya. Duka-duka dai sarakuna talatin da ɗaya ne.
the king of Tirzah, one; all the kings [are] thirty-one.

< Yoshuwa 12 >