< Yohanna 5 >

1 Bayan an ɗan jima, sai Yesu ya haura zuwa Urushalima don wani bikin Yahudawa.
After this there was a feast of the Jews; and Jesus went up to Jerusalem.
2 To, a Urushalima akwai wani tafki kusa da Ƙofar Tumaki, wanda a yaren Arameyik ake kira Betesda an kuma kewaye shi da shirayi biyar.
Now there is at Jerusalem by the sheep [market] a pool, which is called in the Hebrew tongue Bethesda, having five porches.
3 A nan naƙasassu da yawa sukan kwanta, makafi, guragu, shanyayyu.
In these lay a great multitude of impotent folk, of blind, halt, withered, waiting for the moving of the water.
4
For an angel went down at a certain season into the pool, and troubled the water: whosoever then first after the troubling of the water stepped in was made whole of whatsoever disease he had.
5 Akwai wani da yake nan ba shi da amfani shekara talatin da takwas.
And a certain man was there, which had an infirmity thirty and eight years.
6 Da Yesu ya gan shi kwance a can ya kuma sami labari cewa ya daɗe a wannan hali, sai ya tambaye shi, “Kana so ka warke?”
When Jesus saw him lie, and knew that he had been now a long time [in that case], he saith unto him, Wilt thou be made whole?
7 Marar amfanin nan ya ce, “Ranka yă daɗe, ba ni da wanda zai taimaka yă sa ni a cikin tafkin sa’ad da aka motsa ruwan. Yayinda nake ƙoƙarin shiga, sai wani yă riga ni.”
The impotent man answered him, Sir, I have no man, when the water is troubled, to put me into the pool: but while I am coming, another steppeth down before me.
8 Sai Yesu ya ce masa, “Tashi! Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.”
Jesus saith unto him, Rise, take up thy bed, and walk.
9 Nan take mutumin ya warke; ya ɗauki tabarmarsa ya yi tafiya. A ranar da wannan ya faru ranar Asabbaci ce,
And immediately the man was made whole, and took up his bed, and walked: and on the same day was the sabbath.
10 saboda haka kuwa Yahudawa suka ce wa mutumin da aka warkar, “Yau Asabbaci ne; doka ta hana ka ɗauki tabarmarka.”
The Jews therefore said unto him that was cured, It is the sabbath day: it is not lawful for thee to carry [thy] bed.
11 Amma ya amsa ya ce, “Mutumin da ya warkar da ni shi ya ce mini, ‘Ɗauki tabarmarka ka yi tafiya.’”
He answered them, He that made me whole, the same said unto me, Take up thy bed, and walk.
12 Sai suka tambaye shi suka ce, “Wane ne wannan da ya ce maka ka ɗauke ta ka yi tafiya?”
Then asked they him, What man is that which said unto thee, Take up thy bed, and walk?
13 Mutumin da aka warkar kuwa bai ma san ko wane ne ba ne, gama Yesu ya ɓace cikin taron da yake can.
And he that was healed wist not who it was: for Jesus had conveyed himself away, a multitude being in [that] place.
14 Daga baya Yesu ya same shi a haikali ya ce masa, “Ga shi, ka warke. Ka daina yin zunubi, in ba haka ba wani abin da ya fi wannan muni zai iya samunka.”
Afterward Jesus findeth him in the temple, and said unto him, Behold, thou art made whole: sin no more, lest a worse thing come unto thee.
15 Sai mutumin ya je ya gaya wa Yahudawa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
The man departed, and told the Jews that it was Jesus, which had made him whole.
16 To, domin Yesu yana yin waɗannan abubuwa a ranar Asabbaci, sai Yahudawa suka tsananta masa.
And therefore did the Jews persecute Jesus, and sought to slay him, because he had done these things on the sabbath day.
17 Yesu ya ce musu, “Ubana yana cikin aikinsa kullum har yă zuwa wannan rana, haka ni ma, ina kan aiki.”
But Jesus answered them, My Father worketh hitherto, and I work.
18 Don haka Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi; ba don yă karya Asabbaci kawai ba, har ma yana ce Allah Ubansa ne, yana mai da kansa daidai da Allah.
Therefore the Jews sought the more to kill him, because he not only had broken the sabbath, but said also that God was his Father, making himself equal with God.
19 Sai Yesu ya ba su wannan amsa cewa, “Gaskiya nake gaya muku, Ɗan ba ya iya yin kome da kansa; yana yin abin da ya ga Ubansa yake yi ne kawai, gama duk abin da Uban yake yi shi ne Ɗan ma yake yi.
Then answered Jesus and said unto them, Verily, verily, I say unto you, The Son can do nothing of himself, but what he seeth the Father do: for what things soever he doeth, these also doeth the Son likewise.
20 Gama Uban yana ƙaunar Ɗan yana kuma nuna masa duk abin da yake yi. I, za ku kuwa yi mamaki, gama zai nuna masa abubuwan da suka fi waɗannan girma.
For the Father loveth the Son, and sheweth him all things that himself doeth: and he will shew him greater works than these, that ye may marvel.
21 Gama kamar yadda Uban yake tā da matattu yake kuma ba su rai, haka ma Ɗan yake ba da rai ga wanda ya ga dama.
For as the Father raiseth up the dead, and quickeneth [them]; even so the Son quickeneth whom he will.
22 Bugu da ƙari, Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya danƙa dukan hukunci a hannun Ɗan,
For the Father judgeth no man, but hath committed all judgment unto the Son:
23 don kowa yă girmama Ɗan kamar yadda yake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan ba ya girmama Uban, da ya aiko shi ke nan.
That all [men] should honour the Son, even as they honour the Father. He that honoureth not the Son honoureth not the Father which hath sent him.
24 “Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ya ji maganata ya kuma gaskata da wanda ya aiko ni yana da rai madawwami ba za a kuma hukunta shi ba; ya riga ya ƙetare daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios g166)
Verily, verily, I say unto you, He that heareth my word, and believeth on him that sent me, hath everlasting life, and shall not come into condemnation; but is passed from death unto life. (aiōnios g166)
25 Gaskiya nake gaya muku, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya zo sa’ad da matattu za su ji muryar Ɗan Allah waɗanda kuwa suka ji za su rayu.
Verily, verily, I say unto you, The hour is coming, and now is, when the dead shall hear the voice of the Son of God: and they that hear shall live.
26 Gama kamar yadda Uban yana da rai a cikinsa, haka ya sa Ɗan yă kasance da rai a cikin kansa.
For as the Father hath life in himself; so hath he given to the Son to have life in himself;
27 Ya kuma ba shi iko yă hukunta domin shi Ɗan Mutum ne.
And hath given him authority to execute judgment also, because he is the Son of man.
28 “Kada ku yi mamakin wannan, gama lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke cikin kaburbura za su ji muryarsa
Marvel not at this: for the hour is coming, in the which all that are in the graves shall hear his voice,
29 su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta za su tashi zuwa ga rai, waɗanda kuma suka aikata mugunta za su tashi zuwa ga hukunci.
And shall come forth; they that have done good, unto the resurrection of life; and they that have done evil, unto the resurrection of damnation.
30 Ni kaɗai dai ba na iya yin kome, ina shari’a ne bisa ga abin da na ji. Shari’ata kuwa mai adalci ce. Gama ba na neman gamsar da kaina, sai dai in gamshi shi wanda ya aiko ni.
I can of mine own self do nothing: as I hear, I judge: and my judgment is just; because I seek not mine own will, but the will of the Father which hath sent me.
31 “In na ba da shaida a kaina, shaidata ba gaskiya ba ce.
If I bear witness of myself, my witness is not true.
32 Akwai wani mai ba da shaida mai kyau a kaina, na kuma san cewa shaidarsa game da ni gaskiya ce.
There is another that beareth witness of me; and I know that the witness which he witnesseth of me is true.
33 “Kun aika wajen Yohanna ya kuma yi shaida a kan gaskiya.
Ye sent unto John, and he bare witness unto the truth.
34 Ba cewa ina neman shaidar mutum ba ne; sai dai na faɗi haka ne domin ku sami ceto.
But I receive not testimony from man: but these things I say, that ye might be saved.
35 Yohanna fitila ne da ya ci ya kuma ba da haske, kun kuwa zaɓa ku ji daɗin haskensa na ɗan lokaci.
He was a burning and a shining light: and ye were willing for a season to rejoice in his light.
36 “Ina da shaidar da ta fi ta Yohanna ƙarfi. Gama aikin nan da Uba ya ba ni in kammala, wanda kuwa nake yi, yana ba da shaida cewa Uba ne ya aiko ni.
But I have greater witness than that of John: for the works which the Father hath given me to finish, the same works that I do, bear witness of me, that the Father hath sent me.
37 Uba da ya aiko ni kuwa kansa ya yi shaida game da ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ko ganin siffarsa ba,
And the Father himself, which hath sent me, hath borne witness of me. Ye have neither heard his voice at any time, nor seen his shape.
38 maganarsa kuwa ba ta zama a cikinku, gama ba ku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
And ye have not his word abiding in you: for whom he hath sent, him ye believe not.
39 Kuna ta nazarin Nassosi da himma don kuna tsammani ta wurinsu ne kuna samun rai madawwami. Nassosin nan ne suke ba da shaida a kaina, (aiōnios g166)
Search the scriptures; for in them ye think ye have eternal life: and they are they which testify of me. (aiōnios g166)
40 duk da haka kun ƙi zuwa wurina domin ku sami rai.
And ye will not come to me, that ye might have life.
41 “Ni ba na neman yabon mutane,
I receive not honour from men.
42 na fa san ku. Na san cewa ba ku da ƙaunar Allah a cikin zukatanku.
But I know you, that ye have not the love of God in you.
43 Na zo a cikin sunan Ubana, ba ku kuwa karɓe ni ba; amma a ce wani dabam ya zo a cikin sunan kansa, za ku karɓe shi.
I am come in my Father’s name, and ye receive me not: if another shall come in his own name, him ye will receive.
44 Ta yaya za ku gaskata in kuna neman yabon junanku, ba kwa kuwa yin ƙoƙarin neman yabon da yake zuwa daga Allah Makaɗaici?
How can ye believe, which receive honour one of another, and seek not the honour that [cometh] from God only?
45 “Kada fa ku yi tsammani zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi.
Do not think that I will accuse you to the Father: there is [one] that accuseth you, [even] Moses, in whom ye trust.
46 Da a ce kun gaskata da Musa, da kun gaskata ni, domin ya rubuta game da ni.
For had ye believed Moses, ye would have believed me: for he wrote of me.
47 Amma da yake ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, yaya za ku gaskata maganata?”
But if ye believe not his writings, how shall ye believe my words?

< Yohanna 5 >