< Yohanna 11 >
1 To, an yi wani mutum mai suna Lazarus wanda ya yi rashin lafiya. Shi daga Betani ne, ƙauyen su Maryamu da’yar’uwarta Marta.
Byl pak nemocen nějaký Lazar z Betany, z městečka Marie a Marty, sestry její.
2 Maryamun nan kuwa, wadda ɗan’uwanta Lazarus yake rashin lafiya, ita ce ta zuba wa Ubangiji turare ta kuma goge ƙafafunsa da gashin kanta.
A to byla ta Maria, kteráž pomazala Pána mastí, a vytřela nohy jeho vlasy svými, jejíž bratr Lazar byl nemocen.
3 Saboda haka’yan’uwansa mata suka aika da saƙo wa Yesu cewa, “Ubangiji, wannan da kake ƙauna yana rashin lafiya.”
Tedy poslaly k němu ty sestry, řkouce: Pane, aj, ten, kteréhož miluješ, nemocen jest.
4 Sa’ad da ya ji haka, sai Yesu ya ce, “Wannan rashin lafiya ba zai kai ga mutuwa ba. A’a, sai dai don a ɗaukaka Allah a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurin wannan.”
A uslyšav to Ježíš, řekl: Nemoc ta není k smrti, ale pro slávu Boží, aby oslaven byl Syn Boží skrze ni.
5 Yesu kuwa yana ƙaunar Marta da’yar’uwarta da kuma Lazarus.
Miloval pak Ježíš Martu i sestru její i Lazara.
6 Duk da haka sa’ad da ya ji Lazarus ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu a inda yake.
A jakž uslyšel, že by nemocen byl, tedy pozůstal za dva dni na tom místě, kdež byl.
7 Sai ya ce wa almajiransa, “Mu koma Yahudiya.”
Potom pak dí učedlníkům: Poďme zase do Judstva.
8 Sai suka ce, “Rabbi, ba da daɗewa ba ne Yahudawa suka nemi su jajjefe ka, duk da haka za ka koma can?”
Řekli jemu učedlníci: Mistře, nyní hledali tě Židé kamenovati, a zase tam chceš jíti?
9 Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa’a goma sha biyu ce yini guda ba? Mutumin da yake tafiya da rana ba zai yi tuntuɓe ba gama yana ganin hasken duniyan nan.
Odpověděl Ježíš: Zdaliž není dvanácte hodin za den? Chodí-li kdo ve dne, neurazí se; nebo světlo tohoto světa vidí.
10 Sai a sa’ad da yake tafiya da dare ne zai yi tuntuɓe, don ba shi da haske.”
Pakliť by kdo chodil v noci, urazíť se; nebo světla není v něm.
11 Bayan ya faɗa haka, sai ya ƙara ce musu, “Abokinmu Lazarus ya yi barci, amma za ni in tashe shi.”
To pověděl, a potom dí jim: Lazar, přítel náš, spí, ale jduť, abych jej ze sna probudil.
12 Almajiransa suka ce, “Ubangiji, in barci ne yake, to, ai, zai sami sauƙi.”
I řekli učedlníci jeho: Pane, spí-liť, zdráv bude.
13 Yesu kuwa yana magana mutuwarsa ce, amma almajiransa suka ɗauka yana nufin barcin gaskiya ne.
Ale Ježíš řekl o smrti jeho, oni pak domnívali se, že by o spání sna mluvil.
14 Saboda haka sai ya gaya musu a fili cewa, “Lazarus ya mutu,
Tedy řekl jim Ježíš zjevně: Lazar umřel.
15 amma saboda ku na yi farin ciki da ba na can, domin ku gaskata. Amma mu dai je wurinsa.”
A raduji se pro vás, že jsem tam nebyl, abyste věřili. Ale poďme k němu.
16 Sai Toma (wanda ake kira Didaimus) ya ce wa sauran almajiran, “Mu ma mu je, mu mutu tare da shi.”
I řekl Tomáš, kterýž slove Didymus, spoluučedlníkům: Poďme i my, abychom zemřeli s ním.
17 Da isowarsa, Yesu ya tarar Lazarus ya riga ya yi kwana huɗu a kabari.
Přišel tedy Ježíš, a nalezl ho již čtyři dni v hrobě pochovaného.
18 Betani bai kai mil biyu ba daga Urushalima,
Byla pak Betany blízko od Jeruzaléma, okolo honů patnácte.
19 Yahudawa da yawa kuwa suka zo wurin Marta da Maryamu don su yi musu ta’aziyya, saboda rasuwar ɗan’uwansu.
Mnozí pak z Židů byli přišli k Martě a Marii, aby je těšili pro bratra jejich.
20 Sa’ad da Marta ta ji cewa Yesu yana zuwa, sai ta fita don ta tarye shi, amma Maryamu ta zauna a gida.
Tedy Marta, jakž uslyšela, že Ježíš jde, vyšla proti němu, ale Maria doma seděla.
21 Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ubangiji, da kana nan da ɗan’uwana bai mutu ba.
I řekla Marta Ježíšovi: Pane, kdybys ty byl zde, bratr můj byl by neumřel.
22 Amma na san cewa ko yanzu ma Allah zai ba ka duk abin da ka roƙa.”
Ale i nyníť vím, že cožkoli požádal bys od Boha, dá tobě Bůh.
23 Yesu ya ce mata, “Ɗan’uwanki zai sāke tashi.”
Dí jí Ježíš: Vstaneť bratr tvůj.
24 Marta ta amsa ta ce, “Na sani zai sāke tashi a tashin matattu a rana ta ƙarshe.”
Řekla jemu Marta: Vím, že vstane při vzkříšení v den nejposlednější.
25 Yesu ya ce mata, “Ni ne tashin matattu da kuma rai. Duk wanda ya gaskata da ni zai rayu, ko ya mutu;
Řekl jí Ježíš: já jsem vzkříšení i život. Kdo věří ve mne, byť pak i umřel, živ bude.
26 kuma duk wanda yake raye ya kuma gaskata da ni ba zai taɓa mutuwa ba. Kin gaskata wannan?” (aiōn )
A každý, kdož jest živ, a věří ve mne, neumřeť na věky. Věříš-li tomu? (aiōn )
27 Sai ta ce masa, “I, Ubangiji, na gaskata kai ne Kiristi, Ɗan Allah, mai zuwa cikin duniya.”
Řekla jemu: Ovšem, Pane, já jsem uvěřila, že jsi ty Kristus, Syn Boží, kterýž měl přijíti na svět.
28 Bayan ta faɗa haka kuwa, sai ta koma ta je ta kira’yar’uwarta Maryamu a gefe. Ta ce, “Ga Malam ya zo, kuma yana kiranki.”
A když to pověděla, odešla a zavolala tajně Marie, sestry své, řkuci: Mistr zde jest, a volá tebe.
29 Sa’ad da Maryamu ta ji haka sai ta yi wuf ta tafi wurinsa.
Ona jakž uslyšela, vstala rychle, a šla k němu.
30 Yesu dai bai riga ya shiga ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana inda Marta ta tarye shi.
Ještě pak byl Ježíš nepřišel do městečka, ale byl na tom místě, kdež vyšla byla proti němu Marta.
31 Da Yahudawan da suke tare da Maryamu a cikin gida, suke mata ta’aziyya, suka ga ta yi wuf ta fita, sai suka bi ta, suna tsammani za tă kabarin ne tă yi kuka a can.
Tedy Židé, kteříž s ní byli v domě, a těšili ji, viděvše Marii, že rychle vstala a vyšla, šli za ní, řkouce: Jde k hrobu, aby tam plakala.
32 Sa’ad da Maryamu ta kai inda Yesu yake, ta kuma gan shi, sai ta fāɗi a gabansa ta ce, “Ubangiji, da kana nan, da ɗan’uwana bai mutu ba.”
Ale Maria, když tam přišla, kdež byl Ježíš, uzřevši jej, padla k nohám jeho, řkuci jemu: Pane, bys ty byl zde, bratr můj byl by neumřel.
33 Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita ma suna kuka, sai ya yi juyayi ƙwarai a ruhu ya kuma damu.
Ježíš pak jakž uzřel, ana pláče, i Židy, kteříž byli s ní přišli, ani plačí, zastonal duchem, a zkormoutil se.
34 Sai ya yi tambaya ya ce, “Ina kuka sa shi?” Suka amsa suka ce, “Ubangiji zo ka gani.”
A řekl: Kdež jste jej položili? Řkou jemu: Pane, poď a pohleď.
36 Sai Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!”
Tedy řekli Židé: Aj, kterak ho miloval!
37 Amma waɗansunsu suka ce, “Anya, wanda ya buɗe wa makahon nan idanu, ba zai iya yin wani abu yă hana wannan mutum mutuwa ba?”
Někteří pak z nich řekli: Nemohl-liž tento, kterýž otevřel oči slepého, učiniti aby tento neumřel?
38 Yesu, har yanzu cike da juyayi, ya zo kabarin. Kogo ne da aka rufe bakin da dutse.
Ježíš pak opět zastonav sám v sobě, přišel k hrobu. Byla pak jeskyně, a kámen byl svrchu položen na ni.
39 Sai Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Marta,’yar’uwan mamacin ta ce, “Ubangiji, yanzu, ai, zai yi wari, don yau kwanansa huɗu ke nan a can.”
Dí Ježíš: Zdvihněte kámen. Řekla jemu Marta, sestra toho mrtvého: Pane, jižť smrdí; nebo čtyři dni v hrobě jest.
40 Sai Yesu ya ce, “Ban gaya miki cewa in kin gaskata za ki ga ɗaukakar Allah ba?”
Dí jí Ježíš: Všakť jsem řekl, že budeš-li věřiti, uzříš slávu Boží.
41 Saboda haka suka kawar da dutsen. Sa’an nan Yesu ya dubi sama ya ce, “Uba, na gode maka da ka saurare ni.
Tedy zdvihli kámen, kdež byl ten mrtvý pochován. Ježíš pak pozdvihl zhůru očí a řekl: Otče, děkuji tobě, že jsi mne slyšel.
42 Na san kullum kakan saurare ni, na dai faɗa haka ne saboda amfanin mutanen nan da suke tsaitsaye, don su gaskata cewa kai ka aiko ni.”
Já zajisté vím, že mne vždycky slyšíš, ale pro zástup, kterýž okolo stojí, řekl jsem, aby věřili, že jsi ty mne poslal.
43 Sa’ad da ya faɗa haka, sai Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Lazarus, ka fito!”
A to pověděv, zavolal hlasem velikým: Lazaře, poď ven.
44 Sai mamacin ya fito, hannuwansa da ƙafafunsa a daure da ƙyallayen lilin, fuskarsa kuwa an naɗe da mayafi. Yesu ya ce musu, “Ku tuɓe kayan bizo, ku bar shi yă tafi.”
I vyšel ten, kterýž byl umřel, maje svázané ruce i nohy rouchami, a tvář jeho šatem byla obvinuta. Řekl jim Ježíš: Rozvěžtež jej, a nechte, ať odejde.
45 Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo don su ziyarci Maryamu, suka kuma ga abin da Yesu ya yi, suka ba da gaskiya gare shi.
Tedy mnozí z Židů, kteříž byli přišli k Marii, viděvše, co učinil Ježíš, uvěřili v něho.
46 Amma waɗansunsu suka je wurin Farisiyawa suka gaya musu abin da Yesu ya yi.
Někteří pak z nich odešli k farizeům, a pověděli jim, co učinil Ježíš.
47 Sai manyan firistoci da Farisiyawa suka kira taron Majalisa. Suka yi tambaya suna cewa, “Me muke yi ne? Ga mutumin nan yana yin abubuwan banmamaki masu yawa.
I sešli se přední kněží a farizeové v radu, a pravili: Co činíme? Nebo tento člověk divy mnohé činí.
48 In fa muka ƙyale shi ya ci gaba da haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma su zo su karɓe wurinmu su kuma ƙwace ƙasarmu.”
Necháme-li ho tak, všickni uvěří v něho, i přijdou Římané, a odejmou místo naše i lid.
49 Sai waninsu, mai suna Kayifas, wanda ya kasance babban firist a shekarar ya ce, “Ku dai ba ku san kome ba!
Jeden pak z nich, Kaifáš, nejvyšším knězem byv toho léta, řekl jim: Vy nic nevíte,
50 Ba ku gane ba, ai, gwamma mutum ɗaya yă mutu saboda mutane da duk ƙasar ta hallaka.”
Aniž přemyšlujete, že jest užitečné nám, aby jeden člověk umřel za lid, a ne, aby všecken tento národ zahynul.
51 Bai faɗa haka bisa nufinsa ba, sai dai a matsayinsa na babban firist a shekarar, ya yi annabci ne cewa Yesu zai mutu saboda ƙasar Yahudawa,
Toho pak neřekl sám od sebe, ale nejvyšším knězem byv léta toho, prorokoval, že měl Ježíš umříti za tento národ.
52 ba don ƙasan nan kaɗai ba amma don yă tattaro’ya’yan Allah da suke warwatse ma, su zama ɗaya.
A netoliko za tento národ, ale také, aby syny Boží rozptýlené shromáždil v jedno.
53 Saboda haka, daga wannan rana suka ƙulla su ɗauke ransa.
Protož od toho dne radu společně drželi, aby jej zabili.
54 Saboda haka Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba. A maimako haka sai ya janye zuwa yankin kusa da hamada, a wani ƙauye da ake kira Efraim, inda ya zauna da almajiransa.
Ježíš pak již nechodil zjevně mezi Židy, ale odšel odtud do krajiny blízko pouště, do města, kteréž slove Efraim, a tu bydlil s učedlníky svými.
55 Sa’ad da lokaci ya yi kusa a yi Bikin Ƙetarewa na Yahudawa, da yawa suka haura daga ƙauyuka zuwa Urushalima, don su tsarkake kansu kafin Bikin Ƙetarewa.
Byla pak blízko velikanoc Židovská. I šli mnozí do Jeruzaléma z krajiny té před velikonocí, aby se očistili.
56 Suka yi ta neman Yesu, da suke a tsaitsaye a filin haikali kuwa suka dinga tambayar juna, suna cewa, “Me kuka gani? Anya, zai zo Bikin kuwa?”
I hledali Ježíše, a rozmlouvali vespolek, v chrámě stojíce: Co se vám zdá, že nepřišel k svátku?
57 Manyan firistoci da Farisiyawa tuni sun riga sun yi umarni cewa duk wanda ya san inda Yesu yake, yă faɗa don su kama shi.
Vydali pak byli přední kněží a farizeové mandát, jestliže by kdo zvěděl, kde by byl, aby pověděl, aby jej jali.