< Yohanna 1 >

1 Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
In the beginning was the Word, and the Word was with God, and the Word was God.
2 Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
This was in the beginning with God.
3 Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
All things were made by him, and without him not a single creature was made.
4 A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
In him was life, and the life was the light of man.
5 Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
And the light shone in darkness, but the darkness received it not.
6 Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
A man named John, was sent from God.
7 Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
This man came as a witness, to testify concerning the light, that through him, all might believe.
8 Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
He was not himself the light; but came to testify concerning the light.
9 Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
The true light was he who, coming into the world, enlightens every man.
10 Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
He was in the world, and the world was made by him; yet the world knew him not.
11 Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
He came to his own land, and his own people did not receive him;
12 Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
but to as many as received him, believing in his name, he granted the privilege of being children of God;
13 ’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
who derive their birth not from blood, nor from the desire of the flesh, nor from the will of man, but from God.
14 Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
And the Word became incarnate, and sojourned amongst us, (and we beheld his glory, the glory as of the only begotten of the Father, ) full of favor and truth.
15 (Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
(It was concerning him John testified, when he cried, This is He of whom I said, He that comes after me, is preferred to me; for he was before me.)
16 Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
Of his fulness we all have received, even favor for favor's sake;
17 Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
for the law was given by Moses--the favor and the truth came by Jesus Christ.
18 Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
No one ever saw God; it is the only begotten Son, who is in the bosom of the Father, who has made him known.
19 To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
Now this is the testimony of John. When the Jews sent priests and Levites from Jerusalem, to ask him, Who are you?
20 Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
he acknowledged, and denied not, but acknowledged, saying, I am not the Messiah.
21 Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
And they asked him, Who, then? Are you Elijah? He said, I am not. Are you the prophet? He answered, No.
22 A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
They said, Tell, then, who you are, that we may return an answer to them who sent us. What do you say of yourself?
23 Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
He answered, I am he whose voice proclaims in the wilderness, "Make straight the way of the Lord," as said, the Prophet Isaiah.
24 To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
Now they who were sent, were of the Pharisees.
25 suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
And they questioned him further, Why, then, do you immerse, if you be not the Messiah, nor Elijah, nor the prophet?
26 Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
John answered, I immerse in water, but there is one among you whom you know not.
27 Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
It is he who comes after me, and was before me; whose shoe-string I am not worthy to loose.
28 Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
This happened at Bethabara, upon the Jordan, where John was immersing.
29 Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
On the next day, John sees Jesus coming to him, and says, Behold the Lamb of God, that takes away the sin of the world.
30 Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
This is He, concerning whom I said, After me a man comes, who is preferred to me; for he was before me.
31 Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
As for me, I knew him not; but, that he might be made manifest to Israel, I am come immersing in water.
32 Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
John testified further, saying, I saw the spirit descending from heaven, like a dove, and remaining upon him.
33 Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
For my part, I should not have known him, had not He, who sent me to immerse in water, told me, Upon whom you shall see the Spirit descending, and remaining, the same is He who immerses in the Holy Spirit.
34 Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
Having, therefore, seen this, I testify that he is the Son of God.
35 Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
The next day, John, being with two of his disciples,
36 Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
observed Jesus passing, and said, Behold the Lamb of God.
37 Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
The two disciples hearing this, followed Jesus.
38 Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
And Jesus turning about, saw them following, and said to them, What do you seek? They answered, Rabbi, (which signifies Teacher, ) where do you dwell?
39 Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
He replied, Come, and see. They went, and saw where he dwelt, and it being about the tenth hour, abode with him that day.
40 Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
One of the two, who, having heard John, followed Jesus, was Andrew, the brother of Simon Peter.
41 Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
The first he met, was his own brother, Simon; to whom he said, We have found the Messiah, (a name equivalent to Christ.)
42 Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
And he brought him to Jesus. Jesus, looking upon him, said, You are Simon, the son of Jona; you shall be called Cephas, (which denotes the same as Peter.)
43 Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
The next day, he resolved to go to Galilee, and meeting Philip, said to him, Follow me.
44 Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
Now Philip was of Bethsaida, the city of Andrew and Peter.
45 Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
Philip meets Nathanael, and says to him, We have found the person described by Moses in the law, and by the prophets, Jesus, the son of Joseph, of Nazareth.
46 Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
Nathanael says to him, Can any good thing come out of Nazareth? Philip answered, Come and see.
47 Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
Jesus saw Nathanael coming to him, and said, concerning him, Behold an Israelite, indeed, in whom is no guile.
48 Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
Nathanael said to him, Whence do you know me? Jesus answered, I saw you when you were under the fig tree, before Philip called you.
49 Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
Nathanael replying, said to him, Rabbi, you are the Son of God; you are the King of Israel.
50 Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
Jesus answered him, saying, Because I told you that I saw you under the fig tree, you believe!
51 Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”
He added, Most assuredly, I say to you, hereafter you shall see heaven open, and the angels of God ascending from the Son of Man, and descending to him.

< Yohanna 1 >