< Yowel 2 >

1 Ku busa ƙaho a cikin Sihiyona; ku yi karar amo a tsaunina mai tsarki. Bari dukan mazaunan ƙasar su yi rawan jiki, gama ranar Ubangiji tana zuwa. Tana gab da faruwa
Zatrobite na šofar na Sionu in razglasite alarm na moji sveti gori. Naj vsi prebivalci dežele trepetajo, kajti dan Gospodov prihaja, kajti ta je blizu, pri roki;
2 rana ce ta baƙin duhu ƙirin, ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi tana zuwa kamar ketowar alfijir a kan duwatsu yadda ba a taɓa ganin irinta ba, ba kuwa za a ƙara ganin irinta ba har tsararraki masu zuwa.
dan teme in mračnosti, dan oblakov in goste teme se kot jutro razširjajo nad gorami. Veliko ljudstvo in močno, nikoli ni bilo podobnega niti ga ne bo več za tem, celó do let mnogih rodov.
3 A gabansu wuta tana ci, a bayansu ga harshen wuta yana ci, A gabansu ƙasa ta yi kamar gonar Eden, a bayansu kuma jeji ne wofi, babu abin da ya kuɓuce musu.
Ogenj požira pred njimi in za njimi gori plamen. Dežela je pred njimi kakor edenski vrt in za njimi zapuščena divjina; da, in nič jim ne bo pobegnilo.
4 Suna da kamannin dawakai; suna gudu kamar dokin yaƙi.
Njihov videz je kakor videz konjev in kakor konjeniki, tako bodo tekli.
5 Da motsi kamar na kekunan yaƙi sun tsallake ƙwanƙolin duwatsu, kamar ƙarar harshen wuta mai cin tattaka, kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgār yaƙi.
Poskakovali bodo kakor hrup bojnih vozov na vrhovih gora, kakor hrup ognjenega plamena, ki požira strnišče, kakor močno ljudstvo, postavljeno v bojno razvrstitev.
6 Da ganinsu, al’ummai sun kamu da azaba; kowace fuska ta yanƙwane.
Pred njihovim obrazom bo ljudstvo močno zaskrbljeno. Vsi obrazi bodo zbirali črnino.
7 Sukan auka kamar jarumawa; sukan hau katanga kamar sojoji. Kowa yana takawa bisa ga tsari, ba mai kaucewa.
Tekli bodo kakor mogočni možje, obzidje bodo preplezali kakor bojevniki in korakali bodo vsak po svojih poteh in svojih vrst ne bodo pretrgali.
8 Ba sa turin juna, kowane yakan miƙe gaba. Sukan kutsa cikin abokan gāba ba mai tsai da su.
Niti eden ne bo sunil drugega. Hodili bodo vsak po svoji stezi in ko padejo na meč, ne bodo ranjeni.
9 Sukan ruga cikin birni, suna gudu a kan katanga. Sukan hau gidaje, sukan shiga ta tagogi kamar ɓarayi.
Tekali bodo sem ter tja po mestu, tekli bodo na obzidje, splezali bodo na hiše, vstopili bodo pri oknih kakor tat.
10 A gabansu duniya takan girgiza, sararin sama kuma yakan jijjigu, rana da wata su yi duhu, taurari kuma ba sa ba da haske.
Zemlja se bo tresla pred njimi, nebo bo trepetalo, sonce in luna bosta otemnela in zvezde bodo umaknile svoje svetlikanje.
11 Ubangiji ya yi tsawa wa shugaban mayaƙansa; sojojinsa sun fi a ƙirge masu ƙarfi ne kuma su waɗanda suke biyayya da umarninsa. Ranar Ubangiji da girma take; mai banrazana. Wa zai iya jure mata?
Gospod bo izustil svoj glas pred svojo vojsko, kajti njegov tabor je zelo velik, kajti on je močan, ki izvršuje svojo besedo, kajti dan Gospodov je velik in zelo strašen in kdo ga lahko prenese?
12 “Ko yanzu”, in ji Ubangiji, “Ku juyo gare ni da dukan zuciyarku, da azumi da kuka da makoki.”
»Zato se tudi sedaj, « govori Gospod, »obrnite celó k meni z vsem svojim srcem in s postom in z jokom in z žalovanjem
13 Ku kyakkece zuciyarku ba rigunanku ba. Ku juyo ga Ubangiji Allahnku, gama shi mai alheri ne mai tausayi kuma mai jinkirin fushi da yawan ƙauna, yakan kuma janye daga aika da bala’i.
in pretrgajte svoje srce, ne pa svojih oblačil in obrnite se h Gospodu, svojemu Bogu, kajti on je milostljiv in usmiljen, počasen za jezo in velike prijaznosti in se kesa zla.«
14 Wa ya sani? Ko zai juya yă kuma ji tausayi yă sa mana albarka ta wurin hadaya ta gari da hadaya ta sha wa Ubangiji Allahnku.
Kdo ve, če se bo vrnil in pokesal in pustil blagoslov za seboj, celó jedilno daritev in pitno daritev Gospodu, svojemu Bogu?
15 A busa ƙaho a Sihiyona, a yi shelar azumi mai tsarki, a kira tsarkakan taro.
Zatrobite na šofar na Sionu, posvetite post, skličite slovesen zbor,
16 A tattara mutane; ku tsarkake taron; ku kawo dattawa wuri ɗaya; ku kuma tara yara, da waɗanda suke shan mama. Bari ango yă bar ɗakinsa amarya kuma lolokinta.
zberite ljudstvo, posvetite skupnost, zberite starešine, naberite otroke in tiste, ki sesajo pri prsih. Naj pride ženin iz svoje sobe in nevesta iz svoje sobice.
17 Bari firistocin da suke yin hidima a gaban Ubangiji, su yi kuka tsakanin filin haikali da bagade. Bari su ce, “Ka cece mutanenka, ya Ubangiji. Kada ka bar gādonka yă zama abin dariya, da abin ba’a a cikin al’ummai. Me zai sa a ce a cikin mutane, ‘Ina Allahnsu yake?’”
Naj duhovniki, Gospodovi služabniki, jokajo med preddverjem in oltarjem in naj govorijo: »Prizanesi svojemu ljudstvu, oh Gospod in svoje dediščine ne izroči v zasmeh, da bi nad njimi vladali pogani. Zakaj bi med ljudstvom rekli: ›Kje je njihov Bog?‹«
18 Ta haka Ubangiji zai yi kishin ƙasarsa yă kuma ji tausayin mutanensa.
Potem bo Gospod ljubosumen nad svojo deželo in se usmilil svojega ljudstva.
19 Ubangiji zai amsa musu ya ce, “Ina aika da hatsi, sabon ruwan inabi, da mai, isashe da zai ƙosar da ku sosai; ba kuma zan ƙara maishe ku abin dariya ga al’ummai ba.
Da, Gospod bo odgovoril in rekel svojemu ljudstvu: »Glejte, poslal vam bom žito, vino in olje in nasičeni boste s tem in ne bom vas več naredil v zasmeh med pogani,
20 “Zan kori sojojin arewa nesa da ku, in tura su cikin busasshiyar ƙasa marar amfani kuma, kuma da sawunsu na gaba zan tura su zuwa gabashin teku da kuma sawunsu na baya tura su zuwa yammanci a Bahar Rum. Warinsu kuma zai bazu; ɗoyinsu zai tashi.” Tabbatacce ya yi al’amura masu girma.
toda daleč od vas bom odstranil severno vojsko in pregnal jih bom v jalovo in zapuščeno deželo, s svojim obrazom proti vzhodnemu morju in s svojim zadnjim delom proti skrajnemu morju in njegov smrad se bo vzdignil in njegovo zaudarjanje se bo vzdignilo, ker je storil velike stvari.«
21 Kada ki ji tsoro, ya ƙasa; ki yi murna ki kuma yi farin ciki. Tabbatacce Ubangiji ya yi abubuwa masu girma.
Ne boj se, oh dežela, bodi vesela in se raduj, kajti Gospod bo storil velike stvari.
22 Kada ku ji tsoro, ya ku namun jeji, gama wuraren kiwo sun yi kore shar. Itatuwa suna ba da’ya’yansu; itacen ɓaure da na inabi suna ba da amfaninsu.
Ne bodite prestrašene, ve poljske živali, kajti pašniki divjine poganjajo, kajti drevo rodi svoj sad, figovo drevo in trta predajata svojo moč.
23 Ku yi murna, ya ku mutanen Sihiyona, ku yi farin ciki cikin Ubangiji Allahnku, gama ya ba ku ruwan bazara cikin adalci. Yakan aika muku yayyafi a yalwace, na bazara da na kaka, kamar dā.
Bodite torej veseli, vi sionski otroci in veselite se v Gospodu, svojem Bogu, kajti dal vam je zmerno prvi dež in povzročil bo, da vam bo prišel dež, prvi dež in pozni dež v prvem mesecu.
24 Masussukai za su cika da hatsi; randuna za su cika da sabon ruwan inabi da mai suna zuba.
Tla bodo polna pšenice in kadi bodo prekipevale od vina in olja.
25 “Zan mayar muku da abin da fāra suka ci a waɗannan shekaru waɗanda ɗango da fāra masu gaigayewa, da kuma sauran fāra da tarin fāra babban mayaƙan da na aika don su fāɗa muku.
»Povrnil vam bom leta, ki jih je požrla leteča kobilica, škodljiva gosenica, gosenica in kosmata gosenica, moja velika vojska, ki sem jo poslal med vas.
26 Za ku sami a wadace ku ci, har sai kun ƙoshi, za ku kuma yabi sunan Ubangiji Allahnku, wanda ya yi muku ayyukan banmamaki; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
Jedli boste v obilju in boste nasičeni in slavili ime Gospoda, svojega Boga, ki je z vami čudovito ravnal in moje ljudstvo nikoli ne bo osramočeno.
27 Sa’an nan za ku sani ina cikin Isra’ila, cewa ni ne Ubangiji Allahnku, babu wani kuma; mutanena ba za su ƙara shan kunya ba.
Vedeli boste, da sem jaz v Izraelovi sredi in da sem jaz Gospod, vaš Bog in nihče drug, in moje ljudstvo nikoli ne bo osramočeno.
28 “Daga baya kuma, zan zuba Ruhuna a bisan dukan mutane.’Ya’yanku maza da mata za su yi annabci, tsofaffinku za su yi mafarkai, matasanku za su ga wahayoyi.
Potem se bo zgodilo, da bom svojega duha izlil na vse meso. Vaši sinovi in vaše hčere bodo prerokovali, vaši starci bodo sanjali sanje, vaši mladeniči bodo videli videnja.
29 Har ma a bisan bayina, maza da mata, zan zuba Ruhuna a kwanakin nan.
Tudi na služabnike in na pomočnice bom v tistih dneh izlil svojega Duha.
30 Zan nuna abubuwan banmamaki a cikin sammai da kuma a kan duniya, za a ga jini da wuta da murtukewar hayaƙi.
Pokazal bom čudeže na nebu in na zemlji, kri in ogenj in stebre dima.
31 Rana za tă duhunta wata kuma yă zama jini kafin isowar babbar ranan nan mai banrazana ta Ubangiji.
Sonce se bo spremenilo v temo in luna v kri pred velikim in strašnim dnevom Gospodovega prihoda.«
32 Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, gama a Dutsen Sihiyona da Urushalima akwai ceto, a cikin waɗannan da Ubangiji ya kira.
In zgodilo se bo, da kdorkoli bo klical h Gospodovemu imenu, bo osvobojen, kajti osvoboditev bo na gori Sion in v Jeruzalemu, kakor je rekel Gospod in v ostanku, ki ga bo Gospod poklical.

< Yowel 2 >