< Ayuba 9 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Job reprit la parole et dit:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Oui, je sais qu’il en est ainsi: comment l’homme aurait-il gain de cause avec Dieu?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
Si nous désirions discuter avec lui, pas une fois sur mille il ne daignerait nous répondre.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
Eminemment sage, triomphant de force, qui jamais lui tint tête et s’en trouva bien?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
Il déplace les montagnes à l’improviste et les bouleverse dans sa colère.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
Il fait trembler la terre sur ses bases et ébranle les colonnes qui la supportent.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
II donne un ordre au soleil, et le soleil ne paraît point; il met un sceau sur les étoiles.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
A lui seul, il déploie les cieux; il chemine sur la crête des vagues.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
Ila fait la Grande Ourse, l’Orion, les Pléiades et les demeures sidérales du Midi.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
Il accomplit des merveilles sans fin, des prodiges qui ne se peuvent compter.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Ah! S’Il passait auprès de moi, je ne le verrais point; s’il se glissait sous mes yeux, je ne le remarquerais pas.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Quand il empoigne quelqu’un, qui lui fera lâcher prise? Qui lui dira: "Que fais-tu?"
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
Dieu ne refoule pas sa colère; sous ses coups plient les satellites de l’orgueil.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
Et moi j’oserais lui répliquer, je ferais assaut de paroles avec lui,
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
moi, qui tout innocent que je fusse, ne trouverais rien à lui répondre, et demanderais simplement grâce à mon juge!
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Dût-il même se rendre à mon appel, je ne croirais pas qu’il écoute ma voix;
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
car il m’accable sous un vent de tempête et multiplie gratuitement mes blessures.
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Il ne me permet pas de reprendre haleine, tant il m’abreuve d’amertumes.
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
S’Agit-il de faire preuve de force, il est là! S’Agit-il de jugement, il dira: "Qui pourrait m’assigner?"
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Fussé-je innocent, ma bouche me déclarerait coupable! Fussé-je sans reproche, elle me convaincrait de perversité!
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Oui, je suis sans reproche! Je ne me soucie pas de la vie, je suis las de l’existence.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
Tout revient au même: aussi dis-je que juste et méchant, il les fait également périr.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
Si un cataclysme entraîne des morts soudaines, il se rit de l’épreuve des innocents.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
Par lui, la terre a été livrée aux impies: il voile les yeux de ceux qui y rendent la justice. Si ce n’est lui, qui serait-ce?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
Mes jours sont plus rapides qu’un courrier; ils s’enfuient sans avoir vu le bonheur.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
Ils passent comme des barques de jonc, comme l’aigle qui se précipite sur la proie.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
Quand je dis: "Je veux oublier ma souffrance, laisser là ma mine attristée et reprendre mes esprits",
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
je suis envahi par la crainte de mes tourments, sachant bien que tu ne m’absoudras pas.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
Je serai déclaré coupable: pourquoi donc prendre une peine inutile?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
Dussé-je me laver dans de la neige fondue et purifier mes mains avec de la potasse,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
aussitôt tu me plongerais dans une fosse fangeuse, et mes vêtements mêmes auraient horreur de moi.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
Car il n’est pas un homme comme moi pour que je lui réponde et que nous paraissions ensemble en justice.
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
Il n’existe pas d’arbitre entre nous, qui puisse poser sa main sur tous deux.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Qu’il écarte de moi sa verge, et que ses terreurs cessent de peser sur moi.
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Alors je parlerai sans le redouter, car je n’en suis pas là dans le secret de ma conscience.

< Ayuba 9 >