< Ayuba 9 >
Then Job answered and said:
2 “Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
Of a truth, I know that it is so: For how can man be just before God?
3 Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
If he choose to contend with him, He cannot answer him to one charge of a thousand.
4 Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
He is excellent in wisdom, mighty in strength: Who hath hardened himself against him, and prospered?
5 Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
He removeth the mountains, and they know it not; He overturneth them in his anger.
6 Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
He shaketh the earth out of her place, And the pillars thereof tremble.
7 Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
He commandeth the sun, and it riseth not, And he sealeth up the stars.
8 Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
He alone spreadeth out the heavens, And walketh upon the high waves of the sea.
9 Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
He made the Bear, Orion, and the Pleiades, And the secret chambers of the South.
10 Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
He doeth great things past finding out, Yea, wonderful things without number.
11 Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
Lo! he goeth by me, but I see him not; He passeth along, but I do not perceive him.
12 Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
Lo! he seizeth, and who can hinder him? Who will say to him, What doest thou?
13 Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
God will not turn away his anger; The proud helpers are brought low before him.
14 “Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
How much less shall I answer him, And choose out words to contend with him?
15 Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
Though I were innocent, I would not answer him; I would cast myself on the mercy of my judge.
16 Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
Should I call, and he make answer to me, I could not believe that he listened to my voice, —
17 Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
He who falleth upon me with a tempest, And multiplieth my wounds without cause!
18 Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
Who will not suffer me to take my breath, But filleth me with bitterness!
19 In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
If I look to strength, “Lo! here am I!” [[saith he, ]] If to justice, “Who shall summon me to trial?”
20 Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
Though I were upright, yet must my own mouth condemn me; Though I were innocent, He would prove me perverse.
21 “Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
Though I were innocent, I would not care for myself; I would despise my life.
22 Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
It is all one; therefore I will affirm, He destroyeth the righteous and the wicked alike.
23 Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
When the scourge bringeth sudden destruction, He laugheth at the sufferings of the innocent.
24 Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
The earth is given into the hands of the wicked; He covereth the face of the judges thereof; If it be not He, who is it?
25 “Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
My days have been swifter than a courier; They have fled away; they have seen no good.
26 Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
They have gone by like the reed-skiffs; Like the eagle, darting upon his prey.
27 ‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
If I say, I will forget my lamentation, I will change my countenance, and take courage,
28 duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
Still am I in dread of the multitude of my sorrows; For I know that thou wilt not hold me innocent.
29 Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
I shall be found guilty; Why then should I labor in vain?
30 Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
If I wash myself in snow, And cleanse my hands with lye,
31 duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
Still wilt thou plunge me into the pit, So that my own clothes will abhor me.
32 “Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
For He is not a man, as I am, that I may contend with him, And that we may go together into judgment;
33 In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
There is no umpire between us, Who may lay his hand upon us both.
34 wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
Let him take from me his rod, And not dismay me with his terrors,
35 Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.
Then I will speak, and not be afraid of him: For I am not so at heart.