< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Entonces intervino Bildad suhita:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
¿Hasta cuándo hablarás esas cosas, y los dichos de tu boca serán como viento impetuoso?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
¿Él tuerce lo recto? ¿ʼEL-Shadday pervierte la justicia?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Si tus hijos pecaron contra Él, Él los entregó al poder de su transgresión.
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
Si tú buscas a ʼElohim por la mañana e imploras a ʼEL-Shadday,
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
si eres puro y recto, ciertamente ahora se levantará y restaurará tus justos bienes.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
Aunque tu principio sea pequeño, tu final será muy grande.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Te ruego que preguntes a las generaciones pasadas y consideres las cosas investigadas por los antepasados de ellas.
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
Porque nosotros somos de ayer y nada sabemos. Nuestros días sobre la tierra son como una sombra.
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
¿No te instruirán ellos y te hablarán con palabras salidas de su corazón?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
¿El papiro crece donde no hay pantano? ¿Crece el junco sin agua?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Cuando aún están verdes y no están cortados, se secan antes que las otras hierbas.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
Así son las sendas de todos los que olvidan a ʼElohim. Así se desvanece la esperanza del impío,
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
porque su confianza es frágil, y su seguridad como telaraña.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
Si se apoya en su casa, ésta no se sostendrá. Si se aferra a ella, no lo soportará.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Él está verde delante del sol, y por encima de su huerto brota su retoño,
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
aunque sus raíces están entrelazadas sobre un montón de rocas y buscan un lugar entre las piedras.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
Si se arranca de su lugar, éste lo negará: ¡No te vi nunca!
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Ciertamente así es el gozo de su camino. Del polvo brotarán otros.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
Mira, tan ciertamente como ʼElohim nunca sostiene a los malhechores, así nunca se aparta del hombre intachable.
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
Aún llenará tu boca de risa y tus labios con un grito de júbilo.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Los que te aborrecen serán cubiertos de vergüenza. La morada de los impíos desaparecerá.

< Ayuba 8 >