< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Then answered Bildad the Shuhite, and said,
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
How long will you speak these things? and how long shall the words of your mouth be like a strong wind?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Does God pervert judgment? or does the Almighty pervert justice?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
If your children have sinned against him, and he have cast them away for their transgression;
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
If you would seek to God betimes, and make your supplication to the Almighty;
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
If you were pure and upright; surely now he would awake for you, and make the habitation of your righteousness prosperous.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
Though your beginning was small, yet your latter end should greatly increase.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
For inquire, I pray you, of the former age, and prepare yourself to the search of their fathers:
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
(For we are but of yesterday, and know nothing, because our days on earth are a shadow: )
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
Shall not they teach you, and tell you, and utter words out of their heart?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Can the rush grow up without mire? can the flag grow without water?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Whilst it is yet in his greenness, and not cut down, it wither before any other herb.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
So are the paths of all that forget God; and the hypocrite’s hope shall perish:
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
Whose hope shall be cut off, and whose trust shall be a spider’s web.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
He shall lean on his house, but it shall not stand: he shall hold it fast, but it shall not endure.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
He is green before the sun, and his branch shoots forth in his garden.
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
His roots are wrapped about the heap, and sees the place of stones.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
If he destroy him from his place, then it shall deny him, saying, I have not seen you.
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Behold, this is the joy of his way, and out of the earth shall others grow.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
Behold, God will not cast away a perfect man, neither will he help the evil doers:
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
Till he fill your mouth with laughing, and your lips with rejoicing.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
They that hate you shall be clothed with shame; and the dwelling place of the wicked shall come to nothing.

< Ayuba 8 >