< Ayuba 8 >

1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
Toen antwoordde Bildad, de Suhiet, en zeide:
2 “Har yaushe za ka gama faɗa waɗannan abubuwa? Maganganunka ba su da amfani.
Hoe lang zult gij deze dingen spreken, en de redenen uws monds een geweldige wind zijn?
3 Allah ba mai shari’ar gaskiya ba ne? Ko Maɗaukaki yakan yi abin da ba daidai ba?
Zou dan God het recht verkeren, en zou de Almachtige de gerechtigheid verkeren?
4 Lokacin da’ya’yansa suka yi masa zunubi, yakan bar su su sha wahalar da zunubi yake kawowa.
Indien uw kinderen gezondigd hebben tegen Hem, Hij heeft hen ook in de hand hunner overtreding geworpen.
5 Amma in za ka dubi Allah ka roƙi Maɗaukaki,
Maar indien gij naar God vroeg zoekt, en tot den Almachtige om genade bidt;
6 in kai mai tsarki ne, kuma mai adalci, ko yanzu ma zai taimake ka, yă mayar maka iyalinka da farin cikinka.
Zo gij zuiver en recht zijt, gewisselijk zal Hij nu opwaken, om uwentwil, en Hij zal de woning uwer gerechtigheid volmaken.
7 Ko da yake za ka fara da kaɗan, duk da haka za ka gama da samu mai yawa.
Uw beginsel zal wel gering zijn; maar uw laatste zal zeer vermeerderd worden.
8 “Tambayi na gaba da kai ka ji abin da iyayenka suka koya
Want vraag toch naar het vorige geslacht, en bereid u tot de onderzoeking hunner vaderen.
9 gama jiya kaɗai aka haife mu ba mu san kome ba, kuma kwanakinmu a duniya masu wucewa ne.
Want wij zijn van gisteren en weten niet; dewijl onze dagen op de aarde een schaduw zijn.
10 Ba za su bishe ka su kuma gaya maka abin da za ka yi ba? Ba za su yi magana daga cikin hikimar da suke da ita ba?
Zullen die u niet leren, tot u spreken, en uit hun hart redenen voortbrengen?
11 Ko kyauro zai iya yi girma a wurin da ba ruwa? Ko za tă taɓa iya yin girma ba tare da ruwa ba?
Verheft zich de bieze zonder slijk? Groeit het rietgras zonder water?
12 Yayinda take girma ba a yanka ta, takan mutu da sauri fiye da ciyawa.
Als het nog in zijn groenigheid is, hoewel het niet afgesneden wordt, nochtans verdort het voor alle gras.
13 Abin da yake faruwa ke nan da duk wanda yake mantawa da Allah; waɗanda ba su da Allah, ba su da bege.
Alzo zijn de paden van allen, die God vergeten; en de verwachting des huichelaars zal vergaan.
14 Abin da yake dogara a kai ba shi da ƙarfi; abin da yake dogara a kai yanar gizo ce.
Van denwelke zijn hoop walgen zal; en zijn vertrouwen zal zijn een huis der spinnekop.
15 Ya jingina ga yanar gizo, amma ba ta tare shi, sun kama ta, amma ba za tă taimake su tsayawa ba.
Hij zal op zijn huis leunen, maar het zal niet bestaan; hij zal zich daaraan vasthouden, maar het zal niet staande blijven.
16 Yana kama da shukar da aka ba ta ruwa sosai lokacin da akwai rana sosai, tana yaɗuwa da kyau;
Hij is sappig voor de zon, en zijn scheuten gaan over zijn hof uit.
17 shukar tana bin yaɗuwa, jijiyoyinta suna nannaɗe duwatsu, suna neman wurin da za su kama sosai a cikin duwatsu.
Zijn wortelen worden bij de springader ingevlochten; hij ziet een stenige plaats.
18 Amma lokacin da aka tuge shukar daga wurin da take, wurin ba zai san da ita kuma ba, wurin zai ce, ‘Ban taɓa ganin ki ba.’
Maar als God hem verslindt uit zijn plaats, zo zal zij hem loochenen, zeggende: Ik heb u niet gezien.
19 Ba shakka shukar ta mutu ke nan, kuma waɗansu za su tsiro a wurin.
Zie, dat is vreugde zijns wegs; en uit het stof zullen anderen voortspruiten.
20 “Ba shakka, Allah ba ya ƙin marar laifi, ko kuma yă ƙarfafa masu aikata mugunta.
Zie, God zal den oprechte niet verwerpen; Hij vat ook de boosdoeners niet bij de hand;
21 Sai dai yă cika bakinka da dariya, yă sa ka yi sowa ta murna.
Totdat Hij uw mond met gelach vervulle, en uw lippen met gejuich.
22 Maƙiyanka za su sha kunya, za a kawar da tentin mugaye.”
Uw haters zullen met schaamte bekleed worden; en de tent der goddelozen zal niet meer zijn.

< Ayuba 8 >