< Ayuba 40 >

1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
RAB Eyüp'e şöyle dedi:
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
“Her Şeye Gücü Yeten'le çatışan O'nu yola getirebilir mi? Tanrı'yı suçlayan yanıtlasın.”
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
O zaman Eyüp RAB'bi şöyle yanıtladı:
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
“Bak, ben değersiz biriyim, Sana nasıl yanıt verebilirim? Ağzımı elimle kapıyorum.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
Bir kez konuştum, yanıt almadım, İkinci kez konuşamam artık.”
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
RAB kasırganın içinden Eyüp'ü şöyle yanıtladı:
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
“Şimdi erkek gibi kuşağını beline vur da, Ben sorayım, sen anlat.
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
“Adaletimi boşa mı çıkaracaksın? Kendini haklı çıkarmak için beni mi suçlayacaksın?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
Sende Tanrı'nın bileği gibi bilek var mı? Sesin O'nunki gibi gürleyebilir mi?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Öyleyse şan ve şerefe bürün, Görkem ve yücelik kuşan.
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Gazabının ateşini saç, Gururluya bakıp onu alçalt.
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
Gururluya bakıp onu çökert, Kötüleri bulundukları yerde ez.
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Hepsini birlikte toprağa göm, Mezarda yüzlerini kefenle sar.
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
O zaman sağ kolunun seni kurtarabileceğini Ben de kabul ederim.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
“Seninle birlikte yarattığım Behemot'a bak, Sığır gibi ot yiyor.
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
Bak, ne güç var belinde, Karnının kasları ne güçlü!
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
Kuyruğunu sedir ağacı gibi sallıyor, Sımsıkıdır uyluk lifleri.
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
Kemikleri tunç borular, Kaburgaları demir çubuklar gibidir.
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
Tanrı'nın yapıtları arasında ilk sırayı alır, Yalnız Yaratıcısı ona kılıçla yaklaşır.
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
Tepeler ürünlerini ona getirir, Bütün yabanıl hayvanlar yanında oynaşır.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
Hünnap çalıları altında, Kamışlarla örtülü bir bataklıkta yatar.
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
Hünnaplar onu gölgelerinde saklar, Vadideki kavaklar kuşatır.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
Irmak coşsa bile o ürkmez, Güvenlik içindedir, Şeria Irmağı boğazına dayansa bile.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
Gözleri açıkken kim onu tutabilir, Kim kancayla burnunu delebilir?

< Ayuba 40 >