< Ayuba 40 >

1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
Además, Yahvé respondió a Job,
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
“¿Acaso el que discute puede contender con el Todopoderoso? El que discute con Dios, que responda”.
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Entonces Job respondió a Yahvé,
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
“He aquí que soy de poca monta. ¿Qué te voy a responder? Me pongo la mano en la boca.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
He hablado una vez y no voy a responder; Sí, dos veces, pero no seguiré adelante”.
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
Entonces Yahvé respondió a Job desde el torbellino:
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
“Ahora prepárate como un hombre. Te interrogaré, y tú me responderás.
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
¿Acaso anularás mi juicio? ¿Me condenas para justificarte?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
¿O es que tienes un brazo como Dios? ¿Se puede tronar con una voz como la suya?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
“Ahora adórnate con excelencia y dignidad. Arréglate con honor y majestuosidad.
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Derrama la furia de tu ira. Mira a todos los que son orgullosos, y bájalos.
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
Mira a todo el que es orgulloso, y humíllalo. Aplasta a los malvados en su lugar.
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Escóndelos juntos en el polvo. Ata sus rostros en el lugar oculto.
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
Entonces también te admitiré que tu propia mano derecha puede salvarte.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
“Mira ahora el behemoth, que yo he hecho igual que tú. Come hierba como un buey.
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
Mira ahora, su fuerza está en sus muslos. Su fuerza está en los músculos de su vientre.
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
Mueve su cola como un cedro. Los tendones de sus muslos están unidos.
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
Sus huesos son como tubos de bronce. Sus miembros son como barras de hierro.
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
Él es el principal de los caminos de Dios. El que lo hizo le da su espada.
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
Ciertamente, las montañas producen alimento para él, donde juegan todos los animales del campo.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
Se acuesta bajo los árboles de loto, en la cobertura del carrizo, y el pantano.
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
Los lotos lo cubren con su sombra. Los sauces del arroyo lo rodean.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
He aquí que si un río se desborda, no tiembla. Se muestra confiado, aunque el Jordán se hincha hasta la boca.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
Lo tomará cualquiercuando esté de guardia, o atravesar su nariz con un lazo?

< Ayuba 40 >