< Ayuba 40 >
1 Ubangiji ya ce wa Ayuba,
PAN mówił dalej do Hioba:
2 “Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
Czy ten, co wiedzie spór z Wszechmogącym, będzie go pouczał? Niech na to odpowie ten, który strofuje Boga.
3 Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
Wtedy Hiob odpowiedział PANU:
4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
Oto jestem nędzny, cóż ci odpowiem? Przyłożę swoją rękę do ust.
5 Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
Raz mówiłem i drugi, ale [więcej] nie odpowiem, niczego więcej nie dodam.
6 Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
Nadto PAN odpowiedział Hiobowi spośród wichru:
7 “Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
Przepasz teraz swe biodra jak mężczyzna: będę cię pytał, a ty mnie pouczysz.
8 “Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
Czy chcesz wniwecz obrócić mój sąd? Czy potępisz mnie, aby usprawiedliwić samego siebie?
9 Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
Czy masz ramię jak Bóg? Czy zagrzmisz głosem jak on?
10 Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
Ozdób się teraz w majestat i dostojeństwo, przyoblecz się w chwałę i piękno.
11 Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
Rozlej swój gwałtowny gniew, spójrz na każdego pysznego i poniż go.
12 Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
Spójrz na każdego pysznego i upokórz go, zdepcz niegodziwych na ich miejscu.
13 Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Zakryj ich razem w prochu, zamknij w ukryciu ich oblicza.
14 Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
Wtedy i ja ci wyznam, że twoja prawica może cię wybawić.
15 “Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
Oto behemot, którego stworzyłem wraz z tobą; je trawę jak wół.
16 Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
Oto jego siła jest w jego biodrach, a jego moc w pępku jego brzucha.
17 Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
Rusza swoim ogonem jak cedrem, ścięgna jego bioder są splecione.
18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
Jego kości jak rury spiżowe; jego kości jak drągi żelazne.
19 Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
On jest przednim dziełem Boga. Ten, który go uczynił, sam może na niego natrzeć swoim mieczem.
20 Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
Żywność dostarczają mu góry, gdzie wszystkie polne zwierzęta hasają.
21 Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
Leży pod cienistymi drzewami, w ukryciu trzcin i bagien.
22 Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
Drzewa cieniste osłaniają go cieniem, wierzby potoku otaczają go.
23 Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
Oto wypija rzekę i nie spieszy się, będąc pewny, że może wchłonąć Jordan do swojej paszczy.
24 Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?
Czy można go złapać za oczy albo powrozy przeciągnąć mu przez nozdrza?