< Ayuba 4 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Então Elifaz o temanita respondeu, dizendo:
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
Se tentarmos falar contigo, ficarás incomodado? Mas quem poderia deter as palavras?
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Eis que tu ensinavas a muitos, e fortalecias as mãos fracas;
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
Tuas palavras levantavam aos que tropeçavam, e fortificavas os joelhos que desfaleciam.
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
Mas agora [isso] que aconteceu contigo, tu te cansas; e quando [isso] te tocou, te perturbas.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Por acaso não era o teu temor [a Deus] a tua confiança, e a integridade dos teus caminhos tua esperança?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Lembra-te agora, qual foi o inocente que pereceu? E onde os corretos foram destruídos?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
Como eu tenho visto, os que lavram injustiça e semeiam opressão colhem o mesmo.
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
Com o sopro de Deus eles perecem, e pelo vento de sua ira são consumidos.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
O rugido do leão, a voz do leão feroz, e os dentes dos leões jovens são quebrantados.
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
O leão velho perece por falta de presa, e os filhotes da leoa se dispersam.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
Uma palavra me foi dita em segredo, e meu ouvidos escutaram um sussurro dela.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
Em imaginações de visões noturnas, quando o sono profundo cai sobre os homens,
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
Espanto e tremor vieram sobre mim, que espantou todos os meus ossos.
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
Então um vento passou por diante de mim, que fez arrepiar os pelos de minha carne.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
Ele parou, mas não reconheci sua feição; uma figura estava diante de meus olhos, e ouvi uma voz quieta, [que dizia]:
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
Seria o ser humano mais justo que Deus? Seria o homem mais puro que seu Criador?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
Visto que ele não confia em seus servos, e considera seus anjos como loucos,
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
Quanto mais naqueles que habitam em casas de lodo, cujo fundamento está no pó, e são esmagáveis como a traça!
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
Desde a manhã até a tarde são despedaçados, e perecem sempre, sem que ninguém perceba.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
Por acaso sua excelência não se perde com eles mesmos? Eles morrem sem sabedoria.

< Ayuba 4 >