< Ayuba 4 >
1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Then Eliphaz the Temanite answered, and sayde,
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
If we assay to commune with thee, wilt thou be grieued? but who can withholde himselfe from speaking?
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
Behold, thou hast taught many, and hast strengthened the wearie hands.
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
Thy wordes haue confirmed him that was falling, and thou hast strengthened the weake knees.
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
But now it is come vpon thee, and thou art grieued: it toucheth thee, and thou art troubled.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Is not this thy feare, thy confidence, thy pacience, and the vprightnesse of thy wayes?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Remember, I pray thee: who euer perished, being an innocent? or where were the vpright destroyed?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
As I haue seene, they that plow iniquitie, and sowe wickednesse, reape the same.
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
With the blast of God they perish, and with the breath of his nostrels are they cosumed.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
The roaring of the Lion, and the voyce of the Lionesse, and the teeth of the Lions whelpes are broken.
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
The Lyon perisheth for lacke of pray, and the Lyons whelpes are scattered abroade.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
But a thing was brought to me secretly, and mine eare hath receiued a litle thereof.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
In the thoughtes of ye visions of the night, when sleepe falleth on men,
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
Feare came vpon me, and dread which made all my bones to tremble.
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
And the wind passed before me, and made the heares of my flesh to stande vp.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
Then stoode one, and I knewe not his face: an image was before mine eyes, and in silence heard I a voyce, saying,
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
Shall man be more iust then God? or shall a man be more pure then his maker?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
Beholde, he founde no stedfastnesse in his Seruants, and laid follie vpon his Angels.
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
Howe much more in them that dwell in houses of clay, whose foundation is in the dust, which shalbe destroyed before the moth?
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
They be destroyed from the morning vnto the euening: they perish for euer, without regarde.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
Doeth not their dignitie goe away with them? do they not die, and that without wisdom?