< Ayuba 4 >
1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
Then Eliphaz the Temanite answered Job.
2 “In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
“Could I say a word? I don't want to upset you but who could keep quiet and not respond?
3 Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
You've certainly encouraged many people and supported those who are weak.
4 Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
Your advice has helped those who are stumbling not to fall, and you have strengthened those whose knees are weak.
5 Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
But now you're the one suffering and you're upset.
6 Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
Wasn't it your reverence for God that gave you confidence and your integrity that gave you hope?
7 “Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
Think about it: since when did the innocent die? Since when were good people destroyed?
8 Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
From what I've seen it's those who plant evil and sow trouble who reap the same!
9 A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
A breath from God destroys them; a blast of his anger wipes them out.
10 Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
Lions may roar and growl, but their teeth still break.
11 Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
Even a lion dies from lack of food, and the lioness' cubs are scattered.
12 “Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
A word quietly crept up on me; a whisper reached my ear.
13 Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
Troubling thoughts came to me in nightmares when you fall into a deep sleep.
14 Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
I became terrified and trembled; all my bones were shaking.
15 Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
Then a breath brushed my face and gave me goose-pimples.
16 Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
Something stopped, but I couldn't see its face. My eyes could only make out a shape. It was totally quiet, and then I heard a voice:
17 ‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
‘Can anyone be right before God? Can anyone be pure before their Maker?
18 In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
If he doesn't even trust his servants, and he says his angels make mistakes,
19 to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
how much more does this apply to those who live in these houses made of clay, whose foundations are based on dust, who fall apart like clothing to a moth?
20 Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
Alive in the morning, they are dead by evening. They die, unnoticed.
21 Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’
They are like tent ropes that are pulled up, and they collapse in death. They die without wisdom.’