< Ayuba 38 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba. Ya ce,
respondens autem Dominus Iob de turbine dixit
2 “Wane ne wannan da yake ɓata mini shawarata da surutan wofi?
quis est iste involvens sententias sermonibus inperitis
3 Ka sha ɗamara kamar namiji; zan yi maka tambaya, za ka kuwa amsa mini.
accinge sicut vir lumbos tuos interrogabo te et responde mihi
4 “Kana ina lokacin da na aza harsashen duniya? Gaya mini, in ka sani.
ubi eras quando ponebam fundamenta terrae indica mihi si habes intellegentiam
5 Wane ne ya zāna girmanta? Ba shakka ka sani! Wane ne ya ja layin aunawa a kanta?
quis posuit mensuras eius si nosti vel quis tetendit super eam lineam
6 A kan me aka kafa tushenta, ko kuma wa ya sa dutsen kan kusurwarta,
super quo bases illius solidatae sunt aut quis dimisit lapidem angularem eius
7 yayinda taurarin safe suke waƙa tare dukan mala’iku kuma suka yi sowa don farin ciki.
cum me laudarent simul astra matutina et iubilarent omnes filii Dei
8 “Wane ne ya rufe teku a bayan ƙofofi, lokacin da ya burtsatso daga cikin ciki.
quis conclusit ostiis mare quando erumpebat quasi de vulva procedens
9 Lokacin da na yi wa gizagizai riga na kuma naɗe su a cikin duhu sosai,
cum ponerem nubem vestimentum eius et caligine illud quasi pannis infantiae obvolverem
10 sa’ad da na yi masa iyaka na sa masa ƙofofi da wurin kullewa.
circumdedi illud terminis meis et posui vectem et ostia
11 Sa’ad da na ce ga iyakar inda za ka kai, ga inda raƙuman ruwanka za su tsaya?
et dixi usque huc venies et non procedes amplius et hic confringes tumentes fluctus tuos
12 “Ko ka taɓa ba safiya umarni ko kuma ka sa asuba ta fito,
numquid post ortum tuum praecepisti diluculo et ostendisti aurorae locum suum
13 don ta kama gefen duniya ta kakkaɓe mugaye daga cikinta?
et tenuisti concutiens extrema terrae et excussisti impios ex ea
14 Ƙasa ta sāke siffa kamar laka da aka yi wa hatimi; ta fito a fili kamar riga.
restituetur ut lutum signaculum et stabit sicut vestimentum
15 An hana mugaye haskensu, hannun da suka ɗaga an karya shi.
auferetur ab impiis lux sua et brachium excelsum confringetur
16 “Ko ka taɓa tafiya zuwa maɓulɓulan teku, ko kuma ka taɓa zuwa cikin zurfin lungun teku?
numquid ingressus es profunda maris et in novissimis abyssis deambulasti
17 Ko an taɓa nuna maka ƙofar mutuwa? Ko ka taɓa ganin ƙofar inuwar duhun mutuwa?
numquid apertae tibi sunt portae mortis et ostia tenebrosa vidisti
18 Ko ka gane fāɗin duniya? Gaya mini, in ka san wannan duka.
numquid considerasti latitudines terrae indica mihi si nosti omnia
19 “Ina ne hanyar zuwa gidan haske? Kuma a ina duhu yake zama?
in qua via habitet lux et tenebrarum quis locus sit
20 Ko za ka iya kai su wurarensu? Ka san hanyar zuwa wurin da suke zama?
ut ducas unumquodque ad terminos suos et intellegas semitas domus eius
21 Ba shakka ka sani, gama an riga an haife ka a lokacin! Ka yi shekaru da yawa kana rayuwa.
sciebas tunc quod nasciturus esses et numerum dierum tuorum noveras
22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara ko ka taɓa ganin rumbunan ƙanƙara
numquid ingressus es thesauros nivis aut thesauros grandinis aspexisti
23 waɗanda nake ajiya domin lokacin wahala, domin kwanakin yaƙi da faɗa?
quae praeparavi in tempus hostis in diem pugnae et belli
24 Ina ne hanyar zuwa wurin da ake samun walƙiya, ko kuma inda daga nan ne ake watsa iskar gabas zuwa ko’ina cikin duniya?
per quam viam spargitur lux dividitur aestus super terram
25 Wane ne ya yanka hanyar wucewar ruwa, da kuma hanyar walƙiyar tsawa
quis dedit vehementissimo imbri cursum et viam sonantis tonitrui
26 don ba da ruwa a ƙasar da ba kowa a wurin jeji inda ba mai zama ciki
ut plueret super terram absque homine in deserto ubi nullus mortalium commoratur
27 don a ƙosar da wurin da ya bushe a sa ciyawa ta tsiro a can?
ut impleret inviam et desolatam et produceret herbas virentes
28 Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya zama mahaifin raɓa?
quis est pluviae pater vel quis genuit stillas roris
29 Daga cikin wane ne aka haifi ƙanƙara? Wane ne ya haifi jaura daga sammai
de cuius utero egressa est glacies et gelu de caelo quis genuit
30 lokacin da ruwa ya zama da ƙarfi kamar dutse, lokacin da saman ruwa ya daskare?
in similitudinem lapidis aquae durantur et superficies abyssi constringitur
31 “Za ka iya daure kyakkyawar kaza da’ya’yanta? Ko za ka iya kunce igiyoyin mafarauci da kare da zomo?
numquid coniungere valebis micantes stellas Pliadis aut gyrum Arcturi poteris dissipare
32 Za ka iya tattara taurari bisa ga lokacinsu ko kuma ka bi da beyar da’ya’yanta zuwa waje?
numquid producis luciferum in tempore suo et vesperum super filios terrae consurgere facis
33 Ka san dokokin sammai? Ko za ka iya faɗar dangantakar Allah da duniya?
numquid nosti ordinem caeli et pones rationem eius in terra
34 “Za ka iya tsawata wa gizagizai ka kuma rufe kanka da ambaliyar ruwa?
numquid elevabis in nebula vocem tuam et impetus aquarum operiet te
35 Kai ne kake aika walƙiya da tsawa zuwa inda suke zuwa? Ko suna zuwa wurinka su ce, ‘Ga mu nan mun zo?’
numquid mittes fulgura et ibunt et revertentia dicent tibi adsumus
36 Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
quis posuit in visceribus hominis sapientiam vel quis dedit gallo intellegentiam
37 Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
quis enarravit caelorum rationem et concentum caeli quis dormire faciet
38 sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
quando fundebatur pulvis in terram et glebae conpingebantur
39 “Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
numquid capies leaenae praedam et animam catulorum eius implebis
40 Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
quando cubant in antris et in specubus insidiantur
41 Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
quis praeparat corvo escam suam quando pulli eius ad Deum clamant vagantes eo quod non habeant cibos